Rilwan abokin Malam Abbo shi ya gaji da halin da ake ciki, ya samu Malam Abbo ya ce, "Haba Aliyu meyasa kake haka ne? Baka san haƙuri ba ne ko baka san ƙaddara ba? A haka kana tunanin kana burin mutuwa ka shiga aljanna, bayan iyayen da ake samun aljanna ta sanadinsu kai su kake cusawa baƙin ciki da damuwa, dan Allah Aliyu kayi haƙuri haka nan komai ya wuce."
Malam Abbo da ya zabge a sati guda, kaman wan da yayi cuta, ajiyan zuciya ya sauƙe ya ce, "Rilwan na jima da haƙura, amma. . .