Skip to content
Part 28 of 30 in the Series Yar Karuwa by Harira Salihu Isah

Su Umaima na dawowa, washegari suka kai wa Umma Sabeera ziyara, sun samu ta rame ta ƙwanjame, ta fice a hayyacinta, idan ka ga Umma ba za ka ce ita ba ce, Umaima kuka ta din ga yi kaman ranta zai fice, sai da ƙyar Ummu da Umma suka lallasheta, don su ma da akwai mai rarrashin nasu to tabbas kukan za su yi, don Umma tayi laushi sosai ta jima da yin nadama, ba dan ta shiga wannan hali tayi nadama ba sai dan storon haɗuwanta da Allah, ga shi gidan yari daman an ce da shi gidan gyara halinka, mutane da dama da ta haɗu da su ganin rayuwansu, hakan ya ƙara mata storon Allah, ga shi abin haushin ma namijin da tayi abin akan shi ko leƙo ta bai taɓa yi ba, tana neman watanni kusan huɗu zuwa biyar a kulle

Haka su Ummu suka yi sallama da Umma suka dawo cikin jimami, Umaima hawaye ya ƙi barin zuba a idanuwanta, musamman faɗa da nasihan da Umma ta mata, duk kishin mata na hauka baka isa ka hana abin da Allah ya halarta ba, sannan aka yi wa ƴar Manzon Allah SAW guda abokiyar zama balle kuma kai farar hula, Manzon Allah SAW shi ya mana gata kuma ya yiwa mazan ma gata, dan haka mu rungumi haƙuri da salama a zuciyarmu, domin babu abin da ba zai wuce ba muddin aka yi haƙuri.

Abbaa kuwa shiryawa yayi ya tafi Camaroon, tun da ya ga abin na Danish ba mai ƙarewa bane gwanda ya je da kan sa, yana zuwa kuwa ya din ga yi wa Danish faɗa akan zaman da yayi ya daina zuwa ko weekend, Abbaa ya nuna ɓacin ransa sosai dan kaman zai hana shi aiki a Camaroon ɗin ma gaba ɗaya tun da baya ji, ko mahaifiyar sa da ke kulle baya zuwa duba ta balle kuma su.

Danish haƙuri ya din ga bai wa Abbaa sosai akan wannan weekend ɗin zai dawo insha’Allah, Abbaa yayi addu’an Allah ya yarda, bai sanar da Danish fasa auren Banafsha da aka yi ba, ya fi so idan ya dawo Mubin da kan sa sai ya ji labari.

Washegari Abbaa ya tattara ya dawo, a ranan kuma da yake Laraba, Alhaji Mukhtar ya ƙira sa ya sanar da shi maganan auren Banafsha da za’a yi a Sokoto, Abbaa ya ji ba daɗi sosai tun da a karo na biyu ma an buge yaronsa, wannan ya tabbata babu sa’a kuma Banafsha ba rabonsa ba ce, dan haka fatan alkairi yayi da kuma tabbatar wa da Alhaji insha’Allah za su zo ɗaurin auren.

Mami ma ta ƙira Ummu sun yi magana ta sanar mata, farinciki sosai Ummu tayi tana addu’an Allah sanya alkairi ya sa ɗakinta ne sai mutuwa.

Ko da Abbaa ya tunkari Umma da maganan, sai ya tarar da ita ma abin da za ta faɗa masa kenan, sai abun ya basu dariya duka, suka taya ɗan nasu Danish jimami, sannan suka bi Banafsha da fatan alkairi, Abbaa ya ce su shirya gobe Alhamis sai su wuce Sokoto ɗin.

Da Umaima ta ji labari, ai kasa nistuwa tayi dan daɗi da farinciki, ita ba auren ne ke saka ta farinciki ba illa ganin masoyiyarta da za ta yi, asali ma haushin auren take ji tun da a karo na biyu yayanta Danish ya ƙara faɗuwa a wasan, duk da dai shi ya yiwa kan sa, kuma tana addu’an Allah ya sa wannan kam ya tabbata, kada a yiwa masoyiyarta abin da ya faru a na Malam Abbo, dan sam babu daɗi, Banafsha ma tayi tawakkali da wata ce ba za ta jure har haka ba.

Abbaa sanya wa yayi Ummu ta turo masa Umaima, sannan cikin nistuwa ya mata bayanin mutanen da suka zo neman aurenta, ya ba su izinin nemanta, amma maganan aure ana jiran ta dawo ne daman, dan haka anjima yaron zai zo idan sun dai-daita, zuwa gobe kamun su wuce Sokoto zai ƙirata ya ji amsar ta.”

Umaima cikin kunya ta ce, “To Abbaa.”

Abbaa ya ce, “Allah ya miki albarka Ummul-khultum, ta shi kije ko, Allah sanya alkairi ya tabbatar da duk alkairin da ke stakaninku.”

Umaima a zuciya ta amsa da Ameen ta tashi ta tafi, ta faɗa duniyar tunanin Dr Arshan, yanzu idan wani ne daban ya za ta yi? Ita har ga Allah ba ruwanta da Dr yana da mata shi take so, amma kuma bata isa ta ƙi yiwa mahaifinta biyayya ba, addu’an alkairi ita ɗin ma tayi, ta fara shirya kayanta na tafiya Sokoto, tana jiran zuwan baƙonta, amma gefe guda na zuciyarta na mata babu daɗi sosai Dr Arshan zai ce ta yaudare sa.

Ana sallahn Magrib sai ga ƙiran Abbaa, ya turo a faɗa wa Umaima ta fito baƙon nata ya iso, haka Umaima ta shirya staf abin ta, ta fito ta nufi palourn Abbaa dan a can aka sauƙi baƙon nata.

Da sallama Umaima ta shiga palourn kan ta a ƙasa, amma muryan wan da ta ji ya amsa mata sallaman shi ya sanya ta ɗagowa, kallon-kallo suka fara stakaninta da Dr Arshan, har bata san lokacin da ta washe masa talatin da biyunta ba(haƙora), kuma ta kasa ƙarisawa ta zauna.

Dr Arshan stadadden murmushinsa ya sakar mata tare da ɗaga gira guda ya ce, “Hajiyata ko na iso na ƙariso da ke ne?”

Ɗan hararansa Umaima tayi tare da ƙarisawa ta samu kujeranta ta zauna abin ta, zuciyanta cike da farinciki wato Dr ne har ya turo mutanensa, lallai da gaske yake yi, in ta ita ne ma bata ƙi a ɗaura juma’an jibi ba, amma a zahiri akan fiskanta ba za ka ga hakan ba, dan ma ɓata fiska tayi.

Dr Arshan kasa haƙuri yayi ya taso ya dawo kujeran da take zaune mai ɗaukan mutum biyu ya zauna, ai take Umaima ta sha jinin jikinta, ba dai wannan likitan ɗan iska bane mai halin wasu barikakkun likitoci, maganansa ne ya kastar mata da zancen zuci da take yi.

Dr Arshan ya ce, “Da fari dai barka da fitowa Hajiyata, ya Abuja fatan kun dawo lafiya? Sannunku da ƙoƙari Allah taimaka ya ƙara basira, fatan ba’a gajiyar mini da ke ba.”

Umaima ganin jikinsu na gogan na juna, sai ta ɗan masta kaɗan dan ta kasa sakewa, fiskanta a ɗan haɗe ta ce, “Duka alhamdulillah.”

Dr Arshan bai wani yi haƙuri ba, abin sa ya leƙa fiskanta kaman mai neman wani abu, ya ce, “To fushin fa Amarya ta? Ko wani laifi nayi ne?”

Umaima taɓe baki tayi ta ce, “Kawai ka turo iyayenka gidanmu ba izini na, kuma ba tare da sanina ba, baka shawarce ni ka ji ra’ayi na ba, ko mun yi magana makamancin haka da kai?”

Dr Arshan gemunsa ya ɗan sosa tare da cewa, “Allah ya hucu zuciyan Hajiyata, naga dai ni da ke duk abu ɗaya ne ai shiyasa, amma kai na bisa wuya na ayi haƙuri, kuma sai da muka yi magana da yaya Farooq tukunna.”

Umaima harara ta aika masa da shi tare da cewa, “Yaushe muka zama ɗaya? Kuma ai ba yaya Farooq bane zuciyata balle ya san abin da ke ciki, kawai za ka kama ka samu Abbaa da magana ba tare da sanina ba, kai da ka ce matarka guda kuma ba za ka mata kishiya ba, dan ba za ka iya adalci ba, kai ba adali ba ne, ko ka manta san da ka faɗa mana haka ni da masoyiya?”

Dr Arshan ai wani dariya ne ya so ƙwace masa, amma yayi ƙoƙari ya danne dan kar ya ƙara ɓata mata rai, ai shi jam nasa domin maganan da ta yi kaɗai ya isar da shi sanin sirrin da ke zuciyarta, wato dai tana son shi amma tana kishi yana da mata, ranan sun ɗauka da gaske ne, sai ya murmusa dan a haka zai tafi da ita sai daga baya ta ga ba haka bane, a hankali ya ce, “Afuwan amaryata, ranan bana cikin hankali na ne, amma tun da na kalleki na dawo hayyacina na tabbatar ni stayayyen namiji ne kuma zan iya adalci, uwar gida kuma ta amince kada ki ji komai, indai na miki shikkenan a ɗaura.”

Umaima hararansa tayi ta tura baki bata ce komai ba, sai can ta ce, “Tashi nidai ka koma kujeranka ka takura mini.”

Dr Arshan wani malalacin murmushi yayi ya ce, “Wai ina so tun yanzu ki fara koyon sabawa da takuran ne, domin ni takurarre ne, sam-sam ban da haƙuri, haka za ki ta haƙuri da ni, don ana aure kuma za ki ga abin da ake nufi da chewing-gum da kuma bita zai-zai.”

“Uhmn!” Kawai Umaima ta faɗa tayi shiru.

Dr Arshan ganin ta ƙi sakewa sai ya ɗan masta, amma dai bai bar kujeran ba, a haka yake ɗan jan ta da hira, tun bata amsawa har ta fara amsawa, nan yake sanar mata da zai yi tafiya, zai je ɗaurin auren abokinsa.

A dawo lafiya ta masa, sun jima suna hira kaman kada su rabu, a ranan ya cire sim card nasa da yake aiki da shi, ya bata wayansa babba mai kuɗin gaske, da ɗaya extra layinsa da baya ƙira da shi, a hakan ma ya haɗa mata da haƙuri wai bai san bata da waya ba, sai ya dawo zai taho mata da nata sabo tayi manage da wannan.

Umaima da kyar da suɗin goshi ta amshi wayan, dan har sai da ya nuna ran sa ya ɓaci, sannan ta amsa tana tura baki ta gode, shi kuma yayi fishi yayi tafiyansa, ta tashi ta koma ciki ta nuna wa Ummu, da Abbaa ya shigo ma aka nuna masa, ya sanya albarka tare da faɗin ta kula sosai, kuma tun da ta amshi abin hannunsa hakan na nufin sun dai-daita, dan haka zai ma iyayen yaron magana a stai da maganan biki akan lokaci.

Ita dai Umaima kunya ta ji ya sanya ta tashi ta shige ɗakinsu, juyi ta din ga yi da stalle ganin babban wayan da ko mafarkin riƙe irinsa bata taɓa yi ba, wai a haka ma ana haɗa mata da haƙuri, lallai mata Allah ya mana baiwa, ai dole mata su dinga haukan kishi, ita dai ta saka wa ranta insha’Allah za ta yi haƙuri da shi da matarsa su zauna lafiya, nan ta fara shige-shige, da mamaki har ta gama duba waya babu photon wata mace, sai dai yarinya ƙarama wacce suke kama sosai kaman dai ƙanwar sa, da kuma photon wasu da alama yayansa ne da mahaifinsu, sai kuma photonanta na lokacin da suka je Kano, ashe bata sani ba shi sai kashe mata pictures yake yi, haka ta din ga murna, tana jin ina ma masoyiyarta na nan, ai da ita za ta fara nunawa, amma ba komai tun da gobe za su Sokoto, ta mata photonan aurenta da wayan.

Umaima na kwance tana lissafo lissafinta ƙira ya shigo da sabon number, wan da ba suna amma kuma App na true caller ya nuna Dr Arshan Ahmad, dan haka ɗauka tayi tana murmushi, tayi sallama.

Dr Arshan a ɗaya ɓangaren amsa sallaman yayi tare da faɗin, “Kinsan na taho ina fushi amma shi ne ko ki ƙira ni, yayi kyau na gode, amma idan ba ki dage ba uwar gida za ta ƙwace miki angonki.”

Ɓata rai Umaima tayi ta ce, “Daman ai mijinta ne, in ta ƙwace ma ba wani abu.”

Dr Arshan jin yanayin da Umaima tayi magana, wannan karon ya kasa ɓoye dariyansa, sosai ya dara har sai da ita ma ta ƙulu tayi fushin, sannan ya stagaita ya din ga lallaɓa ta, shi da ya tafi da fushi a maimakon shi za’a lallaɓa, sai ga shi shiɗin ke lallaɓata, waya suka yi sosai har sai da duk suke dariya kaman ba abin da ya faru, sannan suka yi sallama.

Washe-gari Umaima, Ummu, Ya Sadeeq da yaya babba, su suka shirya tafiya Sokoto da sassafe, aka bar Nana a gidan yaya babba wajan Hindatu matar sa, Abbaa kuma ba zai samu zuwa ba saboda shungulla, ga waje ba nan kusa ba yayi nisa, da Kanon ne ma da sauƙi.

Mota su Umaima suka bi tun ƙarfe shida suka bar cikin Mubi, suka isa jimeta ƙarfe tara, a nan suka samu motan Sokoto, su ne ba su isa Sokoto ba sai kusan goshin asuba, wajan ƙarfe biyu zuwa uku na dare, suna isowa aka turo musu mota daga masarautan ya ɗauke su, ba su ma kwana a park ba.

Da yake Mami bata sanar da Banafsha zuwan su Umaima ba, dan haka bata san da zuwansu ba, tana can tana sharar baccinta, ko da suka iso aka bai wa su yaya babba masauƙinsu, sannann su Ummu suka wuco wajan Mami, sosai Mami tayi farincikin ganinsu, a daren aka kai wa su babban yaya abin ci, su Ummu ma aka kawo musu, suka taɓa suka wasta ruwa, Umaima tambayar Banafsha tayi, Mami ta ce ta huta abin ta, ta fita harkan Banafsha tana can tana bacci ta bari sai zuwa safiya, suna gama komai suka bi lafiyan gado suka kwanta dan huce gajiyan zaman mota, mutum ka wuni curr a zaune sai a hankali.

Washegari su Ummu basu fito da wuri ba, sai wajan ƙarfe goma suka farka, suka wasta ruwa suka karya, sannan Mami ta aika ƙiran Banafsha, eyye! Banafsha na ganin su Ummu tayi wani irin sufa ta faɗa jikin Ummu, sai da Ummu ta ranƙwasheta akan ita amarya ce, ta daina tsalle-stalle haka, stautsayi na saurin hawa kan Amarya, sai da ta gaishe da su Mami da Ummu, sannan suka rumgume juna da Umaima suka fice, cikin farinciki.

Mami bin su tayi da kallo ta ce, “Waɗannan yara biyu sai addu’an shiriya.”

Ummu ta murmusa kawai, suka ci-gaba da hiransu, sannan suka je ta gaggaishe da matan Sarki da Mama Hadiza, ba jimawa aunty A’isha maman Emaan ta iso ita ma da mijinta.

Umaima ta ce, “Masoyiya ki ce kin stinci dami a kala kawai, waye wannan mai sa’an? Kuma meye haɗinku da Sarkin Sokoto.”

A taƙaice Banafsha ta bata labari ai Sarkin shi ne mahaifin Mami, ita kuma ƙanin Alhaji Mukhtar ne babanta, Umaima ta dinga mamaki da kuma farinciki, wato Mami ƴar gata ce har haka, ƙarshe ma ita jinin sarauta ce, amma ta jure rayuwan da suka yi a baya, lallai Mami mace ce mai zuciya, sannan ta taya Banafsha murna finally ta haɗu da babanta, cikin ikon Allah kuma ƙanin Alhaji ne ma ashe, sannan ta tambayi waye angon nasu kuma?

Banafsha ta kuma cewa, “Ni fa wallahi ki bar wani tambayan waye ne, dan ba miji na ɗauke sa ba, bana son sa ba abin da zan yi da shi.”

Dariya Umaima tayi ta ce, “Amma dai halan girgizan leɓe kike masoyiya? Ko da bansan mijin naki ba kuma ban gansa ba to nasan na daban ne shi, mai mallakanki sai ɗan baiwa, kuma idan baki ɗauke sa miji ba, shi ba ruwansa tuni ya cika miki aiki, kika ƙi ba da haɗin kai tuni ya danneki ya ƙwata haƙƙinsa, in hauka kike yo shi hauka yake, zai biya sadaki bai baki banana ba, tun wuri ki shirya wallahi domin idan kika ƙi ba da haɗin kai za ki iya stintar kan ki a asibiti.”

Banafsha harara ta aika wa Umaima tare da jan guntun staki ta ce, “ke fa Allah ya shiryaki wallahi, wai wa ya faɗa miki dole aure sai da iskancin nan ne?”

Dariya Umaima ta kuma yi ta ce, “shiyasa nake mugun ƙaunarki masoyiya, wallahi nayi kewanki saboda abin dariyanki da yawa, to idan wani abu na damunki ki zuba ido ki sha kallo, tuni kika ƙira ni kina faɗa mini ansha daka yan da ya kamata, taɓarya ya kwashe miki stakuwan kai.”

Bugun wasa ta kai wa Umaima ta ce, “Allah ya shiryaki.”

“Ameen ba wan da yaƙi shiriya musammsn akan wannan, dan kibar ƙiransa iskanci sunna ne cass ma kuwa, ni kuwa bani barin Sokoto sai an haɗa mini haɗin da aka baki, domin na fiki buƙata ni mai kishiya, dole na je na goge wa Dr Arshan haddansa”, ta ƙarishe zancen tana dariya.

Banafsha ta ce, “Ke yanzu da gaske aurensa za ki yi?”

Umaima hararan Banafsha tayi ta ce, “A’a ba auransa zan yi ba yaudaransa zan yi, ke staya a nan ana saki a hanya kina kaucewa…….” Nan Umaima ta kwashe labarin komai da aka yi ta bai wa Banafsha, ta nuna mata wayan nata ma da ya bata.

Banafsha ta saka dariya ta ce, “Allah tabbatar da alkairi to Aminiya ta, na taya ki murna.”

Nan suka ci-gaba da hiransu, har suka ƙarasa wajan Majeeder, ai kaman tayi hauka ita ma na farincikin ganin Umaima, nan suka ƙara kacamewa da hira, har Majeeder ke faɗa mata ai yayanta ne mijin, da yake ba su haɗu da Umaima ido da ido a wajan bikin Mami ba, to bata gane sa ba, kuma Banafsha ƴar rainin hankali ta ƙi faɗa mata wan da ya biya wa Mami kuɗin asibiti ne.

Shiri na musamman aka yi wa Banafsha, ta yi kyau ta gaji da kyau, ga shi yau kayan sarauta aka sanya mata, Masha Allah! Kaman ka sace ta ka kwasa a guje, su Umaima ma ba’a bar su a baya ba ita da Majeeder su ne ƙawayen Amarya, mugun haɗewa suka yi, cikin gida wajan su Mami ma an cancare, kowa yayi kyau ya gaji da kyau, da yake gidan sarauta ne ma’aikatan daban, babu wani aiki sai dai kowa ya sha kwalliyansa, masu aikace-aikace suna yi, Emaan ɗin aunty A’isha tana maƙale da Banafsha ita ce little bride(flower girl).

Ana ɗaura aure ƙaran algaita da bushe-bushe ya cika masarautan, zo ka ga ɓangaren angwaye irin haɗewan da suka yi, Abeed da Arshan da kuma sauran abonansu sun ƙi bari ACM ya huta, domin kuwa zolaya da shaƙiyanci ba irin wan da basa masa, dan duk sun san halinsa akan maganan gantalalliya ƴar jagaliya yake son aura Amma ga shi ya ƙare a jikar sarki, basu san wacece Banafsha a fistara ba ta carawa na gida sai master.

Nan suka shigo gida, aka sa Amarya da ta haɗe da alkyabbanta ta fito da ƙawayenta da iyayenta, aka fara ɗaukan photuna, da Mai martaba duka da su Papi su General su Mami, Momsee ce kawai tayi missing da su Suhaila da su Suhail, kuma uwar ango Mom gantalalliya mai storon kishiya.

Umaima ta rasa wani mamaki ɗaya za ta yi a zuciyanta, na ganin Dr Arshan nata a cikin abokanan ango ne, ko kuwa na ganin sojan da suka sha drama da Banafsha a asibiti a matsayin mijin Banafsha, ai sai da ta samu ta ɗan dara kamun hankalinta ya kwanta, jira take a sarara da yin photunan ta kwashewa Banafsha albarka na barinta da tayi a duhu, ashe Tom nata shi ne mijin nata, wa yaga Tom and Jerry an haɗa su aure, lallai akwai kwasan ƴan kallo.

Captain Abeed san da ya ga Faɗima ce amarya sai da ya kasa haƙuri ya kai bakin sa kunnen ACM ya ce, “Dole ka munafurce mu mana, ashe kasan me ka shuka, wannan ce amaryar taka, matar da aka yi aurenta.”

ACM kuwa yana ji ya ja guntun staki tare da yin banza da Abeed, amma ba wan da ya san abin da ma suka tattauna, stakin ma Abeed ɗin ne kawai ya ji.

Shi ma Dr Arshan ɗin mamakin kallon Umaimarsa yake a Sokoto, sannan ga Faɗima da ta ce masa an yi aurenta tun kwanaki a mastayin amarya, shi ma jira yake su masta ya tambayi Abeed ya hakan ta faru, dan yasan ACM ba zai basa amsa ba, Dr Arshan bai san mamakin da yake yi shi ma Abeed ɗin shi yake yi ba.

Ɓangaren Amarya da ango kuwa, tun da photuna ake yi kuma da iyayensu a wajan, dan dole suka nistu ba su raba hali ba, amma kuma duk in aka tashi yin photon muddin suna manne da juna to sai Banafsha ta ja staki ta ce, “Wallahi ka shirya saki na, dan ni ba kai nake so ba.”

ACM Bunayd kuwa yana jin ta amma ko a jikinsa, shi kawai stakin da take yi ne baya so, kuma Insha Allah zai gyarawa bakinta zama, ba za ta kuma masa staki ba, bari abar su daga shi sai ita, za ta sha mamaki.

Haka aka yi photuna aka gama, sannan aka koma da Amarya ciki, angwaye kuma aka wuce reception a nan cikin masarauta, ACM duk iyayin tambayan Abeed da Arshan ko nuna wa yana jin su bai yi ba, su kuma sun kasa bari sai shaƙiyanci suke masa, Abeed ya ce, “Wallahi dai ka ji storon Allah ka kashe wa yarinya aure ka aure ta, sai ka ce an ce maka shi baya son ta ne, ko kuwa ka fi sa dragon ne.”

Dr Arshan ya ce, “Ni kuwa ina yin siyasarka wallahi ACM, dai-dai kenan ba gargada ba ɓata lokaci za ka sha hidima.”

Ko da suka shige gida, Umaima dariya ta din ga yi kaman ba lafiya ta ce, “Masoyiya munafuka, ashe dai da biyu kika mini shiru, kike wani cika baki wai baki son sa, kinsan wanene ashe, kai amma gaskiya abun ya mini daɗi, wannan shi ake ƙira da wani hanin ga Allah baiwa ne, wato ke kin dage sai soja, zai fi cika miki aiki yan da ya kamata akan ustazu ko yayana.”

Banafsha ma banza tayi da Umaima ba ta ce mata komai ba, dan ita haushi take ji da Bunayd ya manna mata hauka, tayi masifanta bai kula ta ba, ji take kaman ta shaƙe kowa ma ya mutu, kuma za su haɗu ne, kamun yayi maganinta sai tayi maganinsa.

Umaima haƙuri ta kasa yi ta ƙira Dr Arshan a waya, faɗa mata yayi kaman tasan abin da yake shirin yi kenan, nan suka soye abin su ya mata bayanin haɗinsa da su Bunayd, ita ma ta faɗa masa ai wancan auren Banafsha ɗin fasa shi aka yi ba’a yi ba.

A ranan aka shirya kai amarya Lagos, Majeeder, Mama Hadiza, Umma Talatu, Ummu da kuma Amarya su za su kai auren Lagos, Mami tana nan gidan Mai martaba tukunna, Adda Habiba ma sakamakon rashin lafiyan da ta fara ba za ta samu zuwa ba, Mama Suwaiba kuma daman ba’a saka ta a kashi, ga ta dai kaman mara rayuwa amma har yau bata mutu ba.

Lokaci nayi Mai martaba ya yiwa Banafsha nasiha sosai, amma ko kuka bata yi ba, a ranta ta riga ta yanke ba za ta wahalar da kan ta ba, tun da ba son da take ba, dole ya sakota ta dawo ta auri wani daban, in ma Mami ta ƙi riƙe ta ko Affa General to za ta dawo Sokoto abin ta.

Mami ma ta yi wa Banafsha nasiha sosai mai shiga jiki, amma Banafsha ko ehem bata yi ba da sunan kuka, har aka kammala komai, suka shige motoci sai airport da zugan ango da na Amarya duka, jirginsu ya ɗaga sai Lagos.

Su babban yaya kuma da yake Mami tayi magana da Papi, tuni aka biya musu nasu kuɗin jirgin suka bi suka koma Mubi, daman ɗaurin auren kawai suka zo halarta, kuma Mami taji daɗi tayi farincikin sosai da zuwansu duk da Abbaa da Danish da Farooq ba su zo ba.

Ana tafiya da Amarya jikin Mama Suwaiba ya stananta, kamun ayi haka da haka sai jijjiga take yi, ba jimawa rai yayi halinsa, nan aka mata sutura sai gidanta na gaskiya, da kuma fatan Allah mata Rahama ya kuma kyauta, duk da kabarinta da aka tona sai da aka samu macizai a ciki, har gudu uku, sai a na ukun ne ba komai sannan aka saka ta, ana mata addu’an Allah ji ƙanta, mu kuwa Allah sa namu ta zo mu cika da Imani, ko da labarin nan ya riske Adda Habiba ba ƙaramin kuka tayi ba cikin nadama, hankalinta ya ƙara tashi, ciwonta ya stananta, ko iya haka sun san sun girbi abinda suka shuka, kuma Allah ba azzalumin bawansa bane, sannan mai saka wa ne ga wan da aka zalunta.

Su Momsee ana can an cakare an shirya komai sai jiran isowan bataliyan masu kawo amarya, lokacin da jirginsu ya sauƙa kuma, mutanen ACM ne suka je ɗaukan su, da wani irin mahaukacin gudu suke tafiya da su, Umaima duk sun sture, Mama Hadiza kasa haƙuri tayi ta yi magana abin ta, ta ce, “Yaron nan ka bi duniya a sannu, duk gudun jirgi bata ƙure duniya ba balle kai mai tafiya a mota, dan haka ka nistu mutane ka ɗauko ba buhuhhuna ba, mutuwar nan dole ne mun sani amma ba ƙaunarta muke ba dan ba daɗi ne da ita ba.”

Duka motan dariya suka yi, har sai da Papi yayi magana wa Abeed ya sa driver’s ɗin suka rage gudu sannan hankalin Mama Hadiza ya kwanta, ta ce za su je su kashe su a banza, in su sun gaji da duniya to su basu gaji ba, wa ya taɓa gudun hauka da amarya a mota idan ba rashin hankali ba.

Lokacin da suka isa victoria island nan fa kallo ya koma sama, domin da suka shige compound na gidan General Mama Hadiza cewa tayi ƙarya ne an bar Nigeria da su a mota, wannan gida ba dai a Nigeria ba, su aunty A’isha duk da suna koɗa kyawun gidan amma ba su fasa dariyan mama Hadiza ba, Majeeder ta ce musu dan ma ba su ga asalin gidan yaya Bunayd ba, wannan na General ne bai kai nasa kyau ba.

Mama Hadiza ta riƙe haɓs ta ce, “Ke Hauwa’u raba mu da maza ki haɗa mu da mata ƴan uwanmu, kada ki ga bamu taɓa zuwa ba ki sa mu a buhu, yo idan gida ya fi wannan kyau ai ko aljannar duniya aka ƙira sa an tauye haƙƙinsa.

Ko da aka yi parking suka fiffito, da bismillah Mama Hadiza ta saka Banafsha sauƙa a motan, suna shiga an viewing nasu ga kiɗa na tashi, dan Momsee ta riga da tayi arranging na komai, da bismillah tare da addu’a Banafsha ta shiga cikin tankamemen haɗaɗɗen palourn Momsee, nan suka yi wa kan su masauƙi, Momsee dan farincikin kaman ta mai da su ciki, haka ta zo ta rungume Banafsha tana mata maraba, su Suhaila su Ramlah su Nabeela duk farinciki kaman ya kar su, suka rungume Banafsha, Mama Hadiza ta ce, “Wannan kam ai gida kika zo Faɗima, ba sai mun ba da amanarki ba, uwarki ce gwaggonki ce, sai ubanki da ƙannenki, dan haka idan wani abu ya faru daban to na tabbata baƙin halinki ne, amma yarinya kaman wacce ke aiki da aljanu ko maita, ta lashewa kowa zuciya kowan sonki yake yi.”

Ummu tana jin su tana dariyan Mama Hadiza da bakinta baya shiru da biye wa jikokinta, Umma Talatu ma dariyan take yi tana jinjina hali mai kyau irin na Mama Hadiza, ba ruwanta kaman ita ce asalin kakar Banafsha ɗin.

In da aka sauƙe su suke, Momsee komai yi take ba ruwanta ita ce uwar amarya ita ce uwar ango, kuma gwaggon ango gwaggon amarya.

Washe-gari asabar aka yi ƴar walima amma babu angwaye, domin suna can gidan ACM a Banana Island.

Wani washe-gari Lahadi kuma aka ɗau su Mama Hadiza aka kai su gidan ACM dan su gani, amma ban da Banafsha, dan Momsee ta ce anan za ta zauna tukunna a sashin Bunayd, sai ya zo ya ɗauke ta su tafi abin su.

Su Mama Hadiza sun yi santin gidan Bunayd kaman kada su fito a ciki, Umma nan wani imani da storon Ubangiji suka ƙara shiganta, lallai hassada ga mai rabo taki ne, abin da yake rabonka fa to rabonka ne ko da kuwa a bakin kura yake, sai ya iso gare ka, ga shi daman rasuwan Mama Habiba ya risketa tun ranar juma’a da suka iso, nan ta fara istigfaru tana mai ƙara neman yafiyan Ubangiji na laifin da suka aikata, suka bi son zuciyarsu.

Washe-gari Monday, General ya cika su da goma sha tara ta arziƙi suka juyo sai Sokoto, Banafsha bata yi kuka ba sai da su Umaima za su tafi, shikkenan fa daga nan ta kama kuka kaman za ta shiɗe, Momsee tayi rarrashi har ta gaji, dan haka tuni tayi ƙiran ACM ya zo yanzu da gaggawa.

Umaima ma tayi kukan gaske, haka suka koma Sokoto har da Majeeder dan ita kam ta zama ƴar Mami, ta ce za ta zauna a gidan ACM idan yayi mata, amma tun da tana da Maminta yanzu ta fasa, ta baro mutan Lagos ta dawo Sokoto wajan maminta idan yayi su koma Kano tare.

Washe-garin da suka koma Ummu da Umaima da aunty A’isha da Mama Hadiza suka hawo jirgi su ma sai Adamawa, bayan ta’aziyan da suka yi wa Mai martaba, Sarki yayi juyin duniya Mama Hadiza ta zauna tukunna su koma da Ramlatu amma ta ƙi, dan haka ba ƙaramin alkairi ya musu ba dukkansu, ya kuma ƙara jinjina musu da godiya.

Aka bar Mami da Majeeder a Sokoto, Adda Habiba tana nan tana fama da ciwo, wasa gaske daga kaman ciwon ƙafa aka mata allura, sai ƙafa ya fara ruɓewa ya fara cinye wa, an duba aka ga daji ne kuma ga suger duka tana da shi, cikin kwanaki kaɗan kamun ayi bakwai ɗin Mama Suwaiba har ƙafanta ya sundumu sum kaman zai fashe, sai wari yake yana fitar da ɗiwa har da stustosti, ganin jikin Adda Habiba ya sa Mami bata tafi ba, har aka yanke ƙafan, kaman ya warke kuma sai ɗaya ƙafan ma ya harbu, Umma Talatu ta sture ba kaɗan ba, Mami kuwa sai da mai martaba ya mata faɗa sannan suka tattaro suka koma Kano ita da ɗiyar ta Majeeder.

Su Ummu suna komawa iyayen Dr Arshan suka turo komai da komai aka stayar da biki wata uku masu zuwa, tuni Umaima aka fara shiri, ga shi suna kan soyewansu, har yau kuma bata san bai da mata ba, ga kuma bikin yaye su tahfiz saura sati Uku.

Amarya da ango kuwa, Banafsha na kan tiƙan kukanta tun tafiyan su Umaima, da Momsee ta ƙira ACM da yake bai san akan me aka masa ƙiran ba cikin gaggawa ya zo, daman shi kaɗai ne a gidan nasa, Abeed da Dr Arshan duk sun riga da sun wuce a ranan su ma, sun ce dinner ya ce ba wata dinner da zai yi.

ACM yana isowa gidan ya haura wajan Momsee, ita kuwa ta ce ya je sashinsa matar sa na can tana kuka ya lallashe ta, ba daɗi raba mutum da ƴan uwansa da ya saba da su.

Ai ACM Bunayd ji yayi kaman ya haɗiye zuciya ya huta, daman akan wannan fistararriyan ne Momsee ta ƙira shi, har ya wani zo da wuri, ƙwafa yayi a zuciyansa kawai, daman shi ba wan da yake nuna wa akwai drama stakaninsa da Banafsha, ita ɗin ce dai ke nuna wa, dan haka amsawa Momsee yayi da babu damuwa ya juya, sashinsa da ya san tana ciki ya nufa, yana tura ƙofan palourn ya shiga da sallama, amma bata palourn, ɗakin da yake jiyo muryanta ya nufa, yana buɗe ƙofan ɗakinsa ya gan ta a kan gado ta haɗa kai da guiwa tana kuka, wani irin haɗe fiska yayi yana faɗin, “Wannan idiot ɗin a ɗaki na?, Ba tare da ya ƙarisa ciki ba ya ce, “Zo ki fice mini a ɗaki ni ba sa’anki ba ne, je ki nemi wani ɗaki dan ba haɗa ɗaki zan yi da ke ba, idiot.”

Banafsha a masifance ta ɗago ta ce, “Ba za’a fita ɗin ba, ka fitar da ni, mtsww”, ta ja staki tare da mai da kan ta cinyanta ta ci-gaba da sheshsheƙan kukanta.”

ACM murmushin gefen baki yayi tare da faɗin, “Good an zo dai-dai wajan, gwanda da kika tuna mini dan na manta, ba ke irin naki kalan tarbiyyan ba kenan yiwa babba staki, to zan ɗaure miki notirin da ya kunce a kan ki, dan na tabbata Mami ba haka ta nuna miki ba, stiran halin kika yi.”

Kan ta a kan cinyarta bata ɗago ba ta ce, “Ka yi abin da za ka yi, ba storonka nake ji ba.”

ACM kulle ƙofan ɗakin yayi ya saka masa key tare da nufanta gadan-gadan yana faɗin, “Hakan ma ya burge ni, zai fi armashi daman idan ba kya storo na”, ya faɗa tare da haurawa kan gadon.

Banafsha da ta ji kulle ƙofan da yayi, amma taurin zuciya ya sanya ta ci-gaba da mitan ta bata ɗago ba, yana haurawa gadon hantan cikinta ya kaɗa, kamun ta yi wani ƙwaƙƙwaran mosti da sunan gudu tuni ACM ya ja ƙafafuwanta ta yi baya ta kwanta flat akan gadon, kamun ta ce wani abu kums ya bi ta ya danne ta, gaba ɗaya jikinsa na kan ta.

Lokacin da jikinsa ya haɗe da jikinta wani irin azababben shock suka ji dukkansu biyu, Banafsha storo ne ya cika ta dan tasan wannan sam-sam bai da mutunci bai da kirki, ɗan iska ne, ga wani iri da take ji ga kuma nauyinsa duka da ya sake mata.

ACM tun da tudun ƙirjin Banafsha da ba bra ya haɗe da nasa, kusan suma yayi, wani irin azababben yanayin da bai taɓa jin kansa ciki ba yake ji, sake mata nauyinsa yayi cikin mugunta, duk da abin da yake ji bai hana sa ƙare wa fiskanta kallo ba tare da kallon cikin idanuwanta ya ce, “Kukan me kike bayan ba kya storo? Ko daman ban ce miki za mu haɗe ba har kin manta, ina dai ni kike ja wa staki, to zan koya miki yacce ake yiwa mijin biyayya yanzun nan kuma ba ɓata lokaci, dan naga kaman kin jima da watsar da wan da aka koya miki a gida, idiot.”

Banafsha duk da nauyinsa da kuma storon da take ciki na kar ya mata wani abun, amma hakan bai sa bakinta ya mutu ba, cike da masifa ta ce, “Wallahi baka isa ka saka ni kuka ba kayi kaɗan, kukan masoyana da nake so nake yi, kuma ka sani ba storon haɗewa da kai nake yi ba, biyayya kuma wan da ya amsa sunan sa miji ake yiwa ba wan da muke miji ba ya rako mazaje duniya, bana son ka bana ƙaunarka ba abin da zan yi da kai mugu, kuma ka tashi mini a jikina Dan Allah ya isa kake taɓawa, ni jikina yafi ƙarfin irinka, ka tashi kamun na maka abin da baka stammani”, duk maganan nan da Banafsha ke yi idanuwanta a kulle take yi, ga storon da ya cika ta, kawai ƙarfin zuciya ne da haushin ACM da take ji, dan maganan ma da ƙyar yake fitowa.

ACM murmushin gefen baki ya kuma yi tare da ɗaukan hannunsa ya ɗaura a goshinta, kistonta da ya yi har fiskanta ya kawar da gashin yana ƙare wa bakin da ke wannan stiwan kallo, yarinyar nan sam bata storonsa ta rena sa, dole ya nuna mata waye shi ko sau ɗaya ne, tana tare da aurensa tana faɗin wasu take so, bari ya raba ta da abin da take taƙama da shi may be za ta san shi ba sa’anta ba ne, a hankali kaman mai raɗa ya ce, “Bari na nuna miki na fi waɗanda suka amsa sunan miji amsa sunan, kaɗan kuma da nayi yanzu idanuwanki zai gane miki, jikinki kuma zai faɗa miki, idan na buɗe kafafuwanki sai ki gwada mini kina da ƙarfin da za ki iya hana ni shiga in da nayi niya, bari na miki abinda ke baki yi stammani ba kamun ke ki mini, idan na miki ciki sai ki je haka na ga mai aurenki a haka..”

Kamun Banafsha ta yi wani yunƙurin buɗe baki da niyan basa amsa, tuni ya haɗe bakinsu, jikinsa duka na jikinta ga hannyenta ya danne da hannayensa, haka ƙafafuwanta, sannan dragon har ya fara mostawa, ba tare da wani damuwa ba Bunayd ya fara sarrafa harshen sa a cikin bakin Banafsha, duk iya yin ta ko mosti bata iya tayi ba, duk mostin da take yi da kan ta ko gizau bai yi ba, cikin ƙwarewa yake shan bakinta ta stigar da yasan ko ita ce duste dole ta mato akan network.

Banafsha ta kasa ko mosti, ta girgiza kai ya ƙi sake mata baki, ji take ma kaman za ta yi amai, ga dakewan zuciya ta ce bai isa ya saka ta kuka ba, duk hawayen da ke zuwa mata ƙoƙari take ta mai da shi, dan ta rantse yayi kaɗan ya saka ta kuka.

Bunayd kuma yana ɗagowa ya sa haƙorinsa ya yage rigan da ke jikinta ji kake ki! An yage riga, daman kuma babu ko arxiƙin bra a jikinta, yana ido biyu da da boob’s nata a zuciyansa ya sauƙe numfashi ya ce, “Milkies, life saver’s”, tuni ya cusa fiskansa a stakankanunsu cikin rikicewa da zaƙuwa.

Banafsha kuwa yana yage mata riga ta stala ihu, shi kuwa ko a jikinsa, faɗi take, “Allah ya isa, Allah ya isa, ɗan iska mugu, wallahi sai ka biya ni jikina, kuma baka isa ka mini komai ba wallahi.”

Bunayd yayi nisa baya jin ƙira tun da ya shaƙi ƙamshin jikin Banafsha, a rikice ya fara zagaye boob’s nata da harshensa yana lashe su ko ta ina, yana wani irin lumshe ido ko abin da take faɗa ma baya saurara, a hankali ya sanya ɗaya a cikin bakinsa cikin ƙwarewa ya fara sha ya ɗaura hannunsa a kan ɗaya yana lagude sa.

***

Ehem kar wan da ya ce Uwar batoorl ya haka, mun zo ɓangaren soyayya ne, sunan littafi dai ƴar karuwa dan haka dole wani abun a faɗe sa.

<< Yar Karuwa 27Yar Karuwa 29 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×