Kafin faɗuwar rana maganar ta game rugar fulanin da suke rayuwa a rugar duk sun san abinda ke faruwa.
Hayaniya ce kawai ke tashi ƙofar gidan, matasan fulanin maza faɗi suke, a fito da Nafi su ƙona ta. Inna Hure ce ta leƙo tana masifa, “Ku je ku neme ta wani wuri bubu ita nan”. Ɗaya daga cikin matasan ya ce “A fito mana da ita ko mu shige mu duba da kan mu”.
Rigima ce ta barke tsakanin samarin da Inna Hure, ta kasa ta tsare ba wanda zai shiga, suna tsaka da rigima uban yaron. . .