Yabo Da Godiya
Sun tabbata ga Allah (S.W.T) Mai kowa, Mai komai wanda Ya ke sauwake min alamurana ba tare da wani tsumi ko dabarata ba. Ina gaisuwa ga fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (S.A.W) Dan Aminatu da Abdullahi.
Godiya
Gare ku masoyana, makaranta littattafaina dare da rana ina yaba kokarinku, Allah ya bar kaunar da ke tsakaninmu abadan daiman.
*****
A dokance ya shigo gidan, cikin sanda ya ke tafiya zuciyarshi na harbawa da sauri da sauri. Hangota ya yi kwance a kan tabarma. Ya. . .