"Haka kawai bayan yarinya ta gama sanar da kai labarin ta ce wa su ba musulamai ba ne amma har kana iya ce wa zasu zauna a cikin wannan gidan, to wallahi ba zata saɓu ba. Ameera ta faɗa ta na ƙarasowa gurin ranta a mugun ɓace. Kafin Adam ya yi magana ta ci gaba da faɗin "Kasan Allah wannan yarinyar zamanta ya ƙare a wannan gidan dan ubanta, mai za'ayi da dangin tsafi da rashin yin Sallah! Ta na faɗa ta fara kamo Haura da ke ɗuke ta na kuka. Cikin kwantar da murya Adam ya fara faɗin. . .
