Tsabar ɓacin rai muryasa har rawa ta ke yi ya ce "Yanzu abincin da zan ci ɗin shine kika zubar Amera? "Ai muddin ka ce bazan ci abinci a gidan nan ba to sai dai kowa ya huta wallahi "Ameera ta ƙarasa tana miƙewa zata bar gurin. Adam ya ce "Haka kika ce ko? Ta juyo ta ce "Eh haka na ce babu wanda zai ci komai yau. Tana faɗa ta ci gaba da tafiyar ta cike da jin haushin rashin dafa mata Ɗanwaken da take son ci. Sai da ta shige ɗakinta sannan Adam ya iya mi. . .