Ta jeho min tambayar, ƙara duƙƙad da kaina na yi, na fara kuka, a hankali kuma na zayyane mata zamana da Ahmad tun daga samun kwangilar shigo da kayan asibitin Yasmin. Ajiyar zuciya me ƙarfi ta saki, jin na kai ƙarshe, ta ce "Ki ƙara haƙuri, komai zai wuce in sha Allah, babu abinda ya gagari Ubangiji, kema kuma sai kin dage kina tashin dare dan kai ma Allah kukanki.
Baba Karami ni na hana shi shigowa tun a asibiti, dan an ta neman layukan shi a rufe, sai a kira na ƙarshe ni ce na kira kuma. . .