Skip to content
Part 17 of 30 in the Series Fasaha Haimaniyya by Haiman Raees

Al’ummata

Ku mu hankalta

Mu daina mita

Mu ɗau nagarta

Da halin bauta

*****

Bismillahi Allah da ya yo sammai

Shi ya yo bishiya har da fa su ƙassai

Shi ya yi duniya ya ce a bauta mai

Shi ya yi dolaye kana ya yi jarmai

Ya ibadallah ya kamata mu bauta mai

*****

Allah

*****

Tsira da aminci wurinsa abin ƙauna

Manzo habibi ɗaha abin ƙauna

Salati wurinsa ɗa wajen Amina

Shugaban halittu ɗaha abin sona

Ya ibadallah gare shi mu yi biyayya

*****

Manzo

*****

Ya ibadallah gunku na zo yau ni

Ga tunatarwa ga duk mai imani

Gare mu dukka ku har zuwa ni

Ku mu hankalta mu kama addini

In kuma muka ƙi za mu shige tasku

*****

Wayyo

*****

Mai jan kunne kun san dai bai son mu

Baya son mu ko ci gabanmu

Al’adarmu har addininmu

Duka bai son su har da abincinmu

To mu ɗau ɗamara don gyaran kan mu

*****

Bayi

*****

Maimakon haka nan sai muka ɗau wasa

A tsakaninmu muna ta sa-in-sa

Wasu na talla wasu na shan barasa

Ana kashe mu kamar mun zama mussa

To ibadallah ya kamata mu hankalta

*****

Ya fi

*****

Wanda bai son mu shi fa muke ƙyama

Wanda ke son mu sam ba ma sonsa

Rana zafi inuwa na ƙuna

Ga mu nan zaune muna ta hayyasa

To ibadallah ya dai kamata mu hankalta

*****

Ya fi

*****

Ku mu hankalta mu ɗau halin nagarta

Mu daina mita mu koma yin bauta

Ku mu hankalta ku al’ummata

Ku mu ɗau gyara maza duka har mata

In mukai hakan za ko mu rabauta

*****

Bayi

*****

Al’ummata

Ku mu hankalta

Mu daina mita

Mu ɗau nagarta

Da halin bauta

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 5

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Fasaha Haimaniyya 16Fasaha Haimaniyya 18 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×