Wakar Bakandamiya
Wata in har ta fito
Taurari dole su ja da baya
Rana in har ta fito
Tafin hannu bai karewa
*****
Da sunan sarkina
Allah na mai kowa da komai
Wanda ya yi mana rana
Yai ruwa gefe can kuma ga mai
Tsira da amincinsa
Su tabbata a gurin ɗan Amina
Alaye da sahabbansa
Da dukkan mai son Manzona.
*****
Bakandamiya mun danno
Muna nan ko a ina ka duba
Kambu in muka murzo
Saura ai dole su ja da baya
Shi mai nema na jini
Wannan ai sai ya yi can kwata
In. . .
Masha Allah! Godiya muke, Haiman. Allah Ya kara basira da daukaka, Ya bar zumunci, Ya ja kwana.
Amin, Jazakallah Khair
Masha Allah. Allah ya ƙara hazaƙa.
ye
yes