Kusan kullum sai ta kai maganarshi wurin Babana, wai yayi misi kashedi a kaina don lalata ya' yan mutane yake yi, Asabe ma wai ta ki yarda dashi ne yasa ya rabu da ita ya dawo kaina. Sai dai ban san dalili ba, bai ce mata komai ba, nima bai taba yi min wata magana ta kashedi a kan shi ba, ban kuma zaci ya ta ba tunkarar Mubarak din da maganar ba.
Rannan ina zaune a dakina ina jin Babah Lantana tana cewa Babana wai dama ya bayar da rikona ga dangin uwata da suke raina mishi kokarinshi a. . .