A gurguje Halima ta shiga bayi ta watsa ruwa ta fito ta shige ɗakinta, atampa ta zaɓo cikin kayanta ta sanya, ta ɗora zumbulelen hijabinta a sama sannan ta kawo niƙab ta yafa. Baƙin tabarau ɗinta dake ajiye a saman drawer ta ɗauko ta sakaye idanunta, sannan cikin sauri-sauri ta ɗauki agogo ta ɗaure tsintsiyar hannunta na hagu da shi.
Wayarta da 'yar karamar jakarta ta hannu na yashe a saman katifarta ta sunkuya ta ɗauka sannan ta zura takalmanta marasa tudu da suka sha wanki da mai sai sheƙi suke yi.
Ta fito daga. . .