Fitowa Ta Daya
(A ɗakin Delu. Yaran Malam Jatau na kewaye da shi suna tambayar shi yadda ya ƙara ji da jikin)
Sabbinani: Sannu Baba. Allah ya ƙara sauƙi. Ga ruwa ka sha.
Malam Jatau: Amin, na gode sosai ɗan nan.
Talle: Amma Baba, me ya same ka ne haka?
Malam Jatau: Hmm kai dai bari, masifar iyayenku mata ce ta sa na faɗi kamar bani da lafiya. Ba don na yi haka ba da yanzu suna nan suna ta cacar bakin da suka saba. Duk su bi su tayar min da hankali. . . .
Dakyau. Allah ya ƙara basira.