A haka muka wayi gari babu wata mu'amala ta kirki. Sai da muka yi kwana uku a irin wannan halin, ni dai ban sanar da ita matsalata ba. Nayi matukar tausaya mata. a cikon kwana na hudu ne bayan na fita ta buga ma Mukhtar waya ya je gidan, ta sanar dashi halin da muke ciki. Mukhtar daga wajenta bai zame ko'ina ba sai wajena ya yi kokarin in sanar dashi abinda ke faruwa amma ban sanar dashi ba, kai kanka kasan halin Mukhtar ba kasafai yake son matsawa Mutum ya fadi abu ba da son ransa ba. . .