Duk da hakan kokari take yi ta kamo shi, amma ta kasa. Da kyar ya iya mayar da ita gadon, ya tashi da kyar yana numfarfashi.Rarrafawa ya yi ya dauki wayarsa da ta jefar Allah yasa wayar bata fashe ba. Lambar Nuhu ya kira yana magana da kyar. Sai dai har ya sauke maganarsa Nuhu bai fahimci komai ba, kawai dai yasan babu lafiya. Da sauri suka fito shi da matarsa suka shigo dakin. Halin da suka gansu ne yasa ya kira aka tattage su sai asibiti.
Sai dai fa duk yadda aka so a shawo kan matarsa abin. . .