Skip to content
Part 13 of 21 in the Series Miskilin Namiji by Fatima Dan Borno

Sannu a hankali natsuwarsa ke dawowa. Ya sami natsuwar da take neman ya samu. Ya dinga sauke ajiyar zuciya kamar wanda ya ci gudu. Barci ya dinga fizgarsa. Dan haka da taimakonta ya kwanta ta ja masa bargo, tare da tofe shi da addu’a.

Ita kuwa Sakina tana can a labe, jin yadda yake numfarfashi yasakata tunanin tabbas wani abu yake yi da ita. Ta zabura tana cewa,

“Ni ranar girkina sau daya yake yi min, amma ita da yake shafaffiya ce da mai da yaji, gashi can yana sake saduwa da ita. Duk inda munafunci yake mazan nan sun san shi. Allah ya isa hakkina Wallahi, dan bazan taba yafewa ba.”

Samha kuwa zama tayi sosai ta cigaba da kallon hotunan. Akwai hoton kowane yaro na gidan yana jariri da sunansa da date din, amma babu na Zayyad. Wannan ma ya ja hankalinta sosai. Hatta hoton babban dansu da ya rasu, wanda suke ikirarin yayan Zayyad ne, shima gashi nan yana jinjiri, amma babu na Zayyad.

Tana cigaba da kallon hotunan. Abin mamaki da al’ajabi. Hoto ta gani na mutane uku. Alhaji Bako, Alhaji Salisu mahaifin Zayyad, sai kuma Shugaban qasanmu na yanzu Alhaji Mamman.

Gaba dayansu suna dariya cikin farin ciki. Ta sake duba wasu hotunan. Ga Alhaji Mamman nan dauke da jaririn Alhaji Salisu a lokacin da aka haifeshi, wato marigayi Yayan Zayyad. Duk da hoton na da ne, amma kamanninsu ba zai taba canzawa ba. Dukkaninsu ta ganesu. Uwa uba ga sunan kowanne akan saman kansa.

Ta juyo, ta duba ko zata ga Zayyad idonsa biyu. Har yanzu barcinsa yake yi. Ta jinjina kai.

Wata farar takarda ta fado qasa. Ta durkusa ta dauka tare da warware shi.

“Zan baku miliyan dari, amma kada ku kashe min dana da matata.”

Ta karanta rubutun yafi sau a kirga ba ta gane komai ba, dan haka ta nannade ta hada da sauran hotunan, ta jawo drower dinsa ta zube masa komai.

Washegari da sassafe ya shirya ya fice, a sakamakon wani kira na gaggawa da ya samu daga asibitinsu.

Misalin karfe goma sha daya daidai ya fito daga dakin tiyatan, yana sauke numfashi. A hankali ya zare safunan hannunsa ya nufi sink yana wanke hannu.

Daga bayansa ya ji muryar da ya saka shi waiwayowa da sauri.

“Kayi mamakin ganina ko? Yau na zo maka da albishir ne.”

Dr Zayyad ya kafeshi da kyawawan idanunsa yana masa duba na tsanake.

“Ka zauna muyi magana. Kada kayi tunanin nadar maganganuna na saka an kashe min duk wata na’ura da zata iya daukar wata maganata.”

Zayyad bai yi musu ba, ya dawo da baya ya zauna yana dubansa.

“Zayyad! Zabi biyu zan baka a yanzu. Ko ka kashe shugaban kasa a lokacin da zaka yi masa aiki a zuciya, ko kuma Wallahil azim. Daga kan mahaifiyarka kannenka, da kuma amaryarka duk karasasu. Wallahi zan haukataka Zayyad. Zan yi maka abinda zaka tabba tar da ba barazana nake yi maka ba. Da hannunka nake so ka kashe Alhaji Mamman. Ina da hanyoyin da zan iya sakawa a kasheshi, tun daga kan mai kula da shi, zuwa mai bashi abinci. Amma bazan yi hakan ba, kai nake so ka kashe shi da hannayenka.”

Zayyad ya ciga da kallonsa yana mamakin irin wannan abun,

“Tunda kace haka na gane kana da wani boyayyen abu da kakeson aikatawa akaina ne. Alhaji Bako me nayi maka? Me nayi maka da na cancanci irin wannan izayar? Kaine sanadin da raba kwakwalwata da tsohon tunanina na baya. Kai kaine silar wargajewar duk wani farin cikina. Ya zama dole in binciko dalilin da yasa baka kaunar farin cikina, bacin na kasance daya daga cikin wadanda suka auri diyarka.”

Alhaji Bako da zufa ya wanke masa fuska, ya dinga bin Zayyad da kallo, yana jin tsoron ko dai asirinsa ya tonu ne? Zayyad ya cigaba da cewa,

“Zan yi iya kokarina in ga na tuna da abinda ya faru dani a baya. Daga ranar da na tuna, daga wannan ranar ba zaka sake cin galaba akaina ba. Nayi maka wannan alkawarin.”

Har Zayyad ya fice Alhaji Bako bai daina mamakin yadda akayi yasan cewa shi ne silar komai ba.

Da sauri shima ya fice yana saba babbar riga. Alhaji Salisu ya fara kira,

“Sannunka da aiki. Shine zaka gayawa danka ni ne sanadin rabashi da tunaninsa na baya ko? To ka dauka tamkar lokacin tonuwar asirinka ne ya zo.”

Alhaji Salisu ya mike tsaye jikinsa yana rawa,

“Wallahi ban gaya masa komai ba. Haba Alhaji Bako. Meyasa kullum sai ka nemo laifukana ne? Idan zan gayawa Zayyad abubuwan da suka faru kada ka mance nima dole in kwana a ciki.”

Kit! Ya kashe wayar yana kai komo. Diyarsa ya kirawo.

“Sakina ashe ke shashasha ce ban sani ba? Ashe baki da hankali? Tayaya har Zayyad yake bincike akaina duk baki sani ba? Mene ne amfanin zamanki a cikin gidansa? Kin kasa kashe shi, kin kasa samo min komai da zan karu da shi.”

Jikinta yana rawa ta ce,

“Kayi hakuri Abba. Ya datse duk wata hanya ce da zan iya samun wani abu a wurinsa.”

Nan ma katse wayar yayi yana huci.

Layin da ake ta kiransa ya daga a fusace,

“Wai menene?”

“Rankashidade ka kunna tv ka kalli abinda ke faruwa.”

Cikin takaici ya ce,

“Kagaya min kawai bani da tv anan.”

“Magana akeyi akan sace mahaifiyarka da akayi, wai baka damu ba, sannan magana da ka fada akan kudaden da zaka bada karya kake yi.”

Ya jinjina kai.

“Aikin Zayyad ne nasani. Yaron nan ya shirya yin yaqi da ni. Dan haka yanzu wasan zata fara.”

A gajiye ya dawo gida. Yau girkin Sakina ce, dan haka ta fito tana feleke da tray din abinci. Samha ta daga masa hannu, aka ci sa’a ya dago yana dubanta. Ta yi masa alamar da kada ya ci abincin. Ya daga mata gira.

Ta zo ajiyewa kenan, Samha ta dan taba ta, aikuwa da ita da abincin gaba daya suka kife kasa. Sakina ta tashi da sauri tana kallon abincin.

“Dan wulakanci shine zaki tureni?”

Da sauri ta girgiza kai,

“Kiyi hakuri ba da gangar nayi hakan ba.”

Tana tashi ta dauketa da mari. Kafin Zayyad ya tashi, har Samha ta dawo mata da marin.

“Har kin isa ki mareni in kyaleki?”

Sakina ta rike kuncinta.

“Ni kika mara? Yau sai kinsan kin mareni a gidan nan.”

Zayyad ya mike yana dubansu rai a bace,

“Dukkanku ku wuce ku bani waje.”

Samha ta fara wucewa, sannan Sakina ta durkusa tana kwashe abincin. Shi kuma ya ja tsaki ya fice abinsa.

Sai da ya share wasu awanni a waje, sannan ya kirawo Samha a waya.

“Fito farfajiyar gidan nan ina jiranki.”

Mintuna biyar ta yi sai gata ta fito. Ya dubi kyakkyawan fuskarta ya ce,

“Zauna mana.”

Ta dan zauna nesa da shi. Bai ce komai ba, ya cigaba da kallonta.

“Samha meyasa ba zaki yi hakuri bane? Meyasa kike da saurin fushi haka?”

Ta yi banza da shi. Ya tashi da kansa ya dawo kusa da ita.

“Me kika ga ta zuba min a abinci?”

Kuka ke cinta a rai, dan haka ta fashe da kuka. Ya kwantar da kanta a jikinsa yana jin zuciyarsa sam babu dadi.

“Kiyi hakuri. Ni kaina bana jin dadin kaina. Na rasa meke damuna.”

Ta dan sassauta kukan, sannan ta ce,

“Magani naga ta zuba maka, bansan maganin menene ba.”

Ya jinjina kai,

“Na gode Samha. Na gode da kokarin kare lafiyata da kike yi.”

Ta ce,

“Ba saboda kai nake yin hakan ba, saboda mahaifiyata nake haka. Idan na bari ta cutar da kai bansan waye zai kaini wurin Mamana ba.”

Ido ya tsura mata cike da mamakin furucinta. Duk azatonsa tausayinsa take ji, ashe a wurinta ba haka abun yake ba.

Bai ce komai ya cigaba da shafa sassan jikinta. Tun tana basarwa har dukkaninsu yanayinsu ya sauya. Wani abu suke ji kamar sanyi-sanyi duk sai suka fara makale jikinsu. Hannunsa ya cigaba da taba sassan jikinta yana jin wani abu yana sake fizgarsa. A kunne ya rada mata,

“Zo mu je dakina.”

Idanunta a rufe take girgiza kai.

Muryar Sakina da suka ji ne ya dawo da su hayyacinsu.

“Wallahi Dokto sai ka ci wutan Allah. Saboda tsananin zalunci ranar girkina kake irin wannan cin amanar? Wallahi bazan yafe ba.”

Ta wuce tana kuka. Kalmar da ta gaya masa na sai ya ci wutan Allah abin ya dake shi. Da sauri ya juya zai bita, Samha ta riko hannunsa.

“Kada ka tafi ka barni anan, jiri nake gani sosai, bazan iya kai kaina daki ba.”

Dole ya dawo da baya ya riketa tsam a jikinsa. Har dakinta ya kaita bisa kan gado. Ba ta sake shi ba, ba ta kuma daina lumshe idanunta ba. A hankali ya raba ta da hijabin da ta saka. Karamar riga ce a jikinta, hakan ya bashi daman yin tozali da kirjinta. Ya rungumeta tare da saka hannayensa ta baya ya balle maballin bra dinta. Tana ji, sai dai ta kasa hana shi, saboda yanayin da tashiga a yanzu ya wuce misali. Kyawawan kirjinta suka bayyana. Ya fara aika mata sakonni tun daga wuyanta har izuwa kunnenta da ya zira harshensa yana mata wasu abubuwa. Ta sake shige masa sosai, tana sauke numfashi. A lokacin da ya kama ‘yan tagwayenta da tsotso kuwa, sai ta mance gaba daya a duniyar da take. Duk da tana jin dan zafi-zafi, hakan bai hanata sake tura masa kirjin ba, tare da danna kansa. Shi kuwa abin nema ne dama ya samu.

Tana jin yana shirin zarcewa ta rike hannunsa ta saka masa kuka. Dole ya kyaleta tare da rungumeta tsam, “Ya isa haka. Babu abinda zanyi maki.”

Bandakinta ya shiga ya dinga wanke fuskarsa har sai da ya daina ganin jirin, sannan ya fito ya goge kansa da tawul.

Yana bude kofar falon ya tarar da Sakina ta kwanta kasa sosai tana leken qasar kofar Samha.

Tana ganinsa nan da nan ta gigice tana kame-kame. Ya girgiza kai, tare da damkota.

“Me kika ce dazu?”

Bakinta yana rawa ta fara magana, “Dokto kayi hakuri dan Allah.”

Rikon da yayi mata ba na wasa bane, dan tana jin zafin a cikin kasusuwanta,

“Kayi hakuri dan Allah.”

“Uban me kike yi mata a kofar daki? Wallahi Sakina idan baki daina leke da labe ba, watarana sai kin lekowa kanki abinda zai iya kasheki.”

Tana kuka ya shige da ita dakinsa, ya saka key. Tana ganin ya fara raba ta da kayan jikinta ta fahimci akwai abinda yake nema. Farin ciki ya tsirga mata. Ashe zarginsa kawai take yi.

Akanta ya fanshe duk wata bukatarsa da ya dauko daga wurin Samha. Sakina ta sami dukkan gamsuwar da take bukata. Suna gamawa ta hau barci. Ya kafe mummunan fuskarta da kallo, yadda take ta walkiya kamar wacce ta shafa basilin. Ya jinjina kai yana cewa,

“Samha ta fiki komai Sakina.”

Ya sauka yayi wanka ya kimtsa tsaf! Ya tasheta.

“Tashi ki je dakinki ki karasa barcin asarar nan.”

Babu musu ta tashi zata wuce tabar masa kayayyakinta. Ya sake dawo da ita sannan ya nuna mata kayan da idanu,

“Wadannan fa.”

Ba taso da ya ankarar da ita ba, taso tabarsu a wurin har Samha ta gani idan ta zo gyara daki. Haka ta kwashe komai sannan ta fice tana ji aranta tasan me zata yi.

Ya juya  ya fice, tare da kulle kofarsa. A can karkashin zuciyarsa tunani yake yi na yadda zai iya ganin Dokto Sani.

Har ya shiga mota zai tayar, sai kuma ya ji ba zai iya fita ba tare da ya ga Samha ba. Ya sake komawa. Tana nan kwance akan gadon ko hannu ta kasa dagawa. Mamakinsa ya qaru.

Gaba daya ya jawota jikinsa yana cewa,

“Menene? Ko baki da lafiya ne?”

Ta girgiza kai sannan tayi magana cike da shagwaba,

“Jiri nake gani na kasa tashi.”

Ya jinjina kai, sannan ya tashi ya tafi ya tara mata ruwan wanka. Ya kamo hannunta yana cewa,

“Idan kika yi wanka zaki daina ji. Jeki kiyi ina jiranki.”

Da kyar ta iya yin wankan saboda yadda guiwowinta suka yi sanyi.

Ta ji dadin jikinta sosai, dan haka ta saka hijabin jikinta ta fito. Tana ganinsa ta rufe fuskarta da tafukan hannunta alamun kunya. Yayi murmushi kawai tare da cewa,

“Shirya mu je ki rakani asibitin.”

Dama tana so ta fita, dan haka ta kwashi kayanta ta koma bandaki ta shirya. Yana rike da hannunta suka fice.

Kai tsaye Asibitin su Dokto Sani suka nufa. Bayan ya gaisa da wani dokto ne ya tambayeshi ofis dinsa. Ya nuna masa ta inda zai bi ya isa ofishin.

A tsaye yake hannunsa rike da na Samha. Yayi ta kwankwasawa, har dai ya ci sa’a wata ta bude tana kallonsa.

“Dan Allah dokto Sani nake nema.”

Ta girgiza kai,

“Ya bar asibitin nan, kusan kwanaki biyu kenan.”

Ya danyi shiru cike da mamaki,

“Dan Allah idan ba zaki damu ba, ki gaya min asibitin da ya koma.”

Ta yamutsa fuska sannan ta ce,

“Asibitin Aminu Kano.”

Godiya yayi mata ya juya.”

Neman duniyar nan yayiwa Sani a asibitin Aminu Kano babu shi babu dalilinsa.

Haka suka dawo asibiti a gajiye.

Duk inda ya wuce kallonsa akeyi. Mutumin da bai wuce sau biyu aka taba ganinsa da matarsa ba, ita din ma suna tafiya fuskarsa a daure. Yau sai gashi da Samha yana rike da hannunta, fuskarsa kuma babu yabo babu fallasa.

Kai tsaye dakunan marasa lafiya ya shiga. Ya dinga bi yana dudduba su. Daga bisani suka yada zango a ofis dinsa. A kafafunsa ya ajiyeta yana aiki da hannu daya.

Kwankwasa kofa akayi, hakan yasa ya bada izinin a shigo, ba tare da wata damuwa ba. Samha ta yi kokarin ta sauka a jikinsa amma ya hana hakan.

Safiyya ce ta shigo da files. Ganinsu a haka ba karamin daga mata hankali yayi ba. Kanta a kasa ta gama bayaninta jikinta babu inda baya rawa, sannan ta kama hanya zata fice,

“Ke!”

Cak ta tsaya ba tare da juyo ba.

“Ki kiramin Samuel.”

Ta jinjina kai tare da cewa,

“Ok sir.”

A ranar wuni akayi zur ana gulmar Dokto Zayyad. Shi kuwa bayan ya gama kai tsaye suka nufi wurin shakatawa. Suna nan zaune suna ciye-ciyensu,kamar ance Samha ta daga kanta.

“Lahhh… Uncle. duba ka gani ga Dokto Sanin can.”

Karaf! A kunnen Sani. Ya dan waiwayo ya kallesu. Kafin Dokto Zayyad ya dago daga daukar wayarsa da ta subuce ta fadi, sun nemi Dokto Sani ko sama ko kasa basu ganshi ba. Anan kuma sai Zayyad yasha jinin jikinsa,

“Idan da gaske Sani abokina ne, meyasa yake guduna? Hakan ya isa ya tabba tar mini akwai abu a cikin zuciyarsa. Zan nemo shi insha Allahu.”

<< Miskilin Namiji 12Miskilin Namiji 14 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×