Skip to content
Part 23 of 23 in the Series Miskilin Namiji by Fatima Dan Borno

Yau dai Zayyad ya dauki Hajiya Farida da Samha suka nufi wurin shugaban kasa.

Tun shigowar Zayyad asibitin ake bashi girma, har ya isa kofar da za ta sada shi, da dakin shugaban kasa, babu wanda ya hana shi, ko kuma yi masa tambayoyi.

Suna bude kofar suka sami matarsa tana hamshake a wata kujerar alfarma tana latsa waya. Walid da Mufida suma suna zaune a wata kujerar suna latsa laptop.

“Assalamu alaikum.”

Gaba daya suka dago kai. Idanun shugaban kasa fes! Akan Hajiya Farida.

Ita kanta matarsa sai da gabanta ya fadi, duk da babban hoton da ke dakin mijinta hoto ne da aka dauka lokacin can baya, hakan bai hanata gane fuskar Farida ba, domin kuwa manyanta kadai ta kara, har yanzu da kyawunta.

Alhaji Mamman ya yi kokarin tashi jikinsa yana rawa. Da sauri Zayyad ya karaso ya rike shi,

“Daddy kada ka tashi.”

Bakinsa yana rawa ya nunata da hannu.

“Farida! Dama kina raye? Faridata ke ce kika dawo? Don Allah karaso ki tabani in tabbatar da ba mafarkin da na saba yi kullum bane.”

Tana kuka ta karaso da sauri ta rike hannunsa daya tana matsanancin kuka.

Alhaji Mamman ya hade Zayyad da Hajiya Farida ya rike su sosai yana cewa,

“Alhamdulillah! Allah na gode maka, zuri’ata sun dawo. Allah kaine abin godiya. Ka dawo mini da farin cikina. Farida na warke a sallameni in koma in ci gaba da rayuwa da ku.”

Zayyad ya dan saci kallon su Walid dukkaninsu basu ji dadin furucin Alhaji Mamman ba, don haka ya janye kansa, haka Umma ma, ta dan janye tana kokarin tsayar da hawayenta. Ji take yi tamkar an yi mata albishir da gidan aljannah.

Ya juya ya dubi ‘ya’yansa.

“Ku zo ga Yayanku nan Muhseen da mahaifiyarsa.”

Duk cikinsu babu wanda ya yi motsi.

“Hajiya ki zo ki gaisa da Uwargidana Farida.”

Hajiya Samira ta mike tana huci,

“Ban san kana da wata mata bayan ni ba, kuma bana jin ka isa ka mayar da ni amarya a cikin gidan nan. Gwara ka canza tsari. Har ka isa? Dama naga take-takenka tunda wannan tsinannan ya manne maka nasan za a rina. Wato sun ga kana da kudi dole su biyoka domin a ci tare da su. Meya sa lokacin da baka da matsayin nan basu bayyana ba sai yan..”

A fusace Zayyad ya mike,

“Ya isa haka! Ina kudin suke? Yanzu har za ki iya kallona ki ce zan so arzikin ubana? Bacin tun farko ban tashi da mutuwar zuciya irin na ‘ya’yanki ba. Ke kin sani ba a canzawa tuwo suna. Zan dauki mahaifiyata zamu koma, idan ya gama mulkin ya dawo gida insha Allahu zamu dawo kusa da shi. Amma ina so ki sani, ban taba alfahari ba, ina da tarin dukiyar da duk hadamarki da ke da ‘ya’yanki baku isa ku cinye shi ba.”

Ya jawo hannun Umma da nufin ficewa. Alhaji Mamman ya ce,

“Idan har ni mahaifinka ne ina umartarka da kada ka tafi ko ina. It kanta tasani, duk wanda ya rabeni yasan da zamanku.”

Duk da haka zuciya tana cin Zayyad bai fasa yunkurin barin dakin ba.

Umma ta kalle shi da mamaki,

“Kai Muhseen! Yaushe mahaifinka zai yi maka magana har ka kasa bin umarninsa? Alhaji Bako sun cuceni, sun cuci zuri’ata. Tunda har za su iya koya maka dabi’u irin na yahudawa.”

Da sauri ya dawo kusa da ita yana jin kansa yana sarawa. Ita kuwa Hajiya Samira tsoron Zayyad ne ya kama ta, wanda hatta su Walid sun kasa yin wani motsi.

Zayyad ya girgiza kai ya ce,

“Umma Wallahi babu wanda ya bata mini tarbiyya. Bana son duniya ta amince da kalaman Hajiya ne, bana son su yi tunanin tuntuni na sanshi amma ban je gareshi a matsayin dansa ba. Umma bansan Daddy mahaifina bane, sai a dalilin labarin da ya bani, da kuma bincike da na yi. Duk da haka ban amince ba, har sai da na dibi jininsa na hada da nawa aka yi mana D.N.A test sannan na karasa gazgata hakan.”

Dakin ya yi shiru. Alhaji Mamman baya kaunar dalilin da zai raba shi da Dansa, da kuma matarsa. Yana kallon Hajiya da ‘ya’yanta suka bar dakin.

Samha ta karaso ta durkusa har kasa ta gaida shi. Ya dubeta cike da farin ciki,

“Masha Allah. Surukar tawa kenan? Su waye iyayenta?”

Dam! Gabansu ya fadi. Jikin Samha ya yi sanyi. Zayyad yana shirin yin magana, Samha ta yi magana cikin kuka,

“Bani da kowa, bani da dangi.”

Zayyad ya dago yana kallonta kamar ya rungumeta ya lallasheta.

“Kada ki damu, ki daina cewa baki da kowa, mune iyayenki.”

A jiyar zuciya ya kwacewa Zayyad. Ya dan yi mata alamu, don haka suka fice suka bar iyayen su biyu.

Can bayan shuke-shuke ya kaita.

Shi kuwa Alhaji Mamman yana ganin duk sun fita ya rungume matarsa suna sakin ajiyar zuciya.

Zayyad ya kafe wani tsuntsu da idanu, har sai da Samha ta bi shi da kallo.

“Kin ga tsuntsayen can yadda suke soyayya?”

Ba ta yi magana ba, sai “Uhum!” Da ta ce.

Ya jawota gaba daya jikinsa, ya hade fuskokinsu wuri daya, daga bisani ya zura harshensa a cikin bakinta, a hankali ta kama tana tsotso. Ya zare harshensa ya dan manna mata sumba, sannan ya ce,

“Gobe zan kaiki wani wuri mai kyawun gani na tabbata za ki so wurin.”

Anan ma ba ta yi magana ba. Kewar mahaifiyarta kawai take yi, tana son ganin mahaifiyarta kamar yadda Zayyad ya gano iyayensa.

Tsaf ya gama fahimtar abin da ke damunta, don haka ya zabi ya basar kawai.

Washegari aka sallami shugaban kasa kai tsaye gidansa na Kaduna ya ce a wuce da shi, domin Umma ta dage ba za ta zauna a vila ba, ba ta son rigima, gwara ya barta a Kaduna.

Sun sami komai tsaf-tsaf. Sai da ya tsaya ya yi hira da ‘yan jarida ya gaya masu komai akan matarsa da dansa. Duk hoton da za a dauki shugaban kasa, sai fuskar Zayyad da Hajiya Farida ya fito. Da kyar Samha ta tsaya itama akayi hoton da ita.

Cikin abin da bai wuce awanni ba, duniyar yanar gizo ya dauka. Babu maganar da ake yi sai na shugaban kasa. Mutane da dama sun sha mamaki, sun kuma yi tir da hali irin na Alhaji Bako.

Bayan sun shiga gida sun natsa ne, aka bukaci su fito falo a ci abinci.

Samha ta fito kanta a kasa. Kamar an ce ta dago, tana dagowa idanunta suka sauka akan mahaifiyarta. Ta mance a gaban surukai take, ta kwala kara ta nufeta da gudu. Tana rungumeta ta rushe da kuka. Itama Hajiya Aishar kuka take yi da iya karfinta. Babu wanda ya dakatar da su, har suka gaji suka tsahirta. Sai ita Samhar da take yawaita share hawaye idan ya zubo.

  Zayyad ya dubi mahaifinsa ya ce,

“Daddy ka ganeta ko?”

Ya yi murmushi ya ce,

“Idan zan iya manceta, babu shakka zan iya mance iyayen da suka haifeni. Mahaifiyar Alhaji Bako ne.”

Ya jinjina kai, kafin ya labarta masu komai, na yadda ya taimaka masu ita da mahaifiyar Samha.

Idan ban da albarka babu abin da yake sha a falon nan. Ya ci gaba da cewa,

“Zan rike su, zan ci gaba da basu kulawa. Sai dai Mama har yanzu bamu san mene ne alakarki da Alhaji Bako ba, da har yake so ya kasheki.”

Samha ta dubi mamanta. Hajiya Aisha ta gyara zama tana goge kwalla.

“Yana tare da mahaifin Samha ne. Sai ya kwashe kudadensa dukka, da nufin za su yi kasuwanci. Bayan ya kwashe sai kuma ya zo da kansa da yaransa suka kashe shi. Abin da yasa yake neman rayuwata saboda ya nemi takardar yarjejeniyar da suka yi da mahaifin Samha, wanda da sa hannunsa, ni kuma na boye takardar. Shi ne yake so ya kasheni.”

  Hajiya Laure ta saka kuka tana cewa,

“Yaron nan Bako bansan halin wa ya dauko ba. Mahaifinsa ba haka yake ba, ya mayar da kashe mutane tamkar kashe dabbobi. Allah ya isa nonona da ya sha.”

Da sauri Daddy ya ce,

“A’a don Allah Hajiya ki daina yi masa baki, ki barshi ya ji da abubuwan da suke kansa.”

Tare da suka ci abinci aka yi ta hira. Samha dai tana jikin mahaifiyarta. Hatta da aka zo kwanciya dakin mahaifiyarta ta shige tana kwance a jikinta tana cin apple. Zayyad ya yi sallama. Mama ta ce masa ya shigo.

Bayan ya gaidata Mama ta kalleta ta ce,

“Ta shi ku je hirar ta isa haka sai da safe.”

Ta dan saci kallonsa sannan ta rufe idanunta. Zayyad ya mike yana sosa kai. Tun yana sa ran zai ganta har ya hakura ya kwanta. Ita kanta ta yi kewarsa, sai dai kewar ba ta kama kafar na mahaifiyarta ba.

Sai karfe ukun dare Samha ta barsu suka yi barci. Tana makale da mahaifiyarta kamar wani zai kwace ta.

Zayyad ya siyawa Mama da Hajiya Laure gida, suna zaune tare. Tunda dama sun shaku.

Hankalinsa bai kwanta ba, sai da ya ga an daurewa Alhaji Bako hukuncin kisa ta hanyar rataya.

A ranar da aka yanke hukuncin Zayyad ya dinga kallonsa yana masa murmushi.

Shi kansa Zayyad din ya kusa komawa Kaduna gaba daya, da zarar an kammala gina masa babban asibitinsa da ke Kaduna. Yana bukatar zama kusa da mahaifiyarsa.

Sai yau suka samu natsuwa a cikin gidansu.

Karfe tara daidai agogon bangon ya buga, wanda ya yi daidai da shigowar Zayyad da kaji. Tana lullube a gado, ya je ya dauko plate ya zuba masu, sannan ya tasheta ta zo su ci. Kadan ta ci, sannan ta ture ta sake wanko baki, ya ce ta je ta yi alwala.

Ba ta yi musu ba, ta je ta yi. Bayan sun yi Sallah ne ya dafa kanta ya dinga jero mata addu’o’i har sai da ta ji kwalla yana zuba daga idanunta.

Ta riga shi hawa gado ta kudundune.

Ta bayanta ta kwanta gaba daya suka nutse a cikin tattausan gadon suna shakar kamshin juna.

“Na gode da abubuwan da kayi mini. Allah ya biyaka. Yanzu mene ne matsayin aurenmu da muka yi a bisa yarjejeniya?”

Yana murmushi yana lalubarta sannan ya hura mata iska a kunne ya rada mata,

“Yanzu zan gaya maki matsayin aurenmu.”

Ba ta iya magana ba, sai dan rike hannunsa da take yi.

Tana jin yadda yake tsotson kirjinta lamarin da ke kara rikirkitata, ta saka dogayen yatsunta tana shafa gashin kansa, tare da cusa hannun a cikin gashin tana cukuikuishi. Lamarin na yau daban yake da sauran lokaci, a lokacin da ya cire bakinsa, ba ta san lokacin da ta sake mayar da kansa ba.

Da haka ya karasa fitar da ita hayyacinta, har ya ci nasarar yin addu’a. Wani irin zafi ta ji yana shigaarta. Duk da haka ba ta hana shi ba, saboda tana bukatar ya kawar mata da sha’awar da ya taso mata kamar za ta mutu. Duk yadda take zaton lamarin ya wuce tunaninta, ba ta san lokacin da ta fara kuka ba.

  Shi kuma yana iya bakin kokarinsa wurin ganin bai ci zalinta ba. A haka ya mayar da ita cikakkiyar mace.

  Bayan sun natsa ne ya jawota jikinsa yana lallashinta,

“Ki yi hakuri wannan ranar ta fi dukkan ranaku mahimmanci. Ki kwantar da hankalinki ki gode Allah. Samha ba zan iya rabuwa da ke ba, domin ina sonki fiye da komai, ina son duk wani farin cikinki. Ban fara sonki ba, bansan ina sonki ba, har sai da na auroki. Da farko na za ci zan iya rabuwa da ke kamar yadda na gaya maki a baya, sai dai na gane zuciyata ba za ta sami cikakkiyar kwanciyar hankali ba idan babu ke a kusa da ni. Don Allah kada ki gujeni.”

Kalamansa sun ratsata ta yadda har ta daina jin haushinsa. Tana jin yadda yake shafa sassan jikinta har barci ya kwasheta.

Ya rigata yin wanka domin ya tsani kwana da janaba, sannan ya hau kan darduma ya sake kaskantar da kansa yana nema masu zaman lafiya, tare da godiya ga Allah da ya taimaka kasa wajen warwarewar matsalarsa.

   Da asuba shi ya taimaka mata ta yi wankan janaba bayan ya gasa mata jiki. Ya wuce masallaci ya barta tana Sallarta a daki.

Daga masallaci ya wuce ofis domin duba wasu marasa lafiya. Daga can ya wuce gidan Alhaji Salisu a karo na farko tun samun matsalolin baya.

A falo ya same su dukkaninsu suna karyawa.

Nura da Sharifat suka mike tsaye duk suna kallonsa. Babu wanda ya yi zaton zai sake waiwayansu.

Ya karaso cikin takunsa na isa, ya karaso gaban Umma ya durkusa har kasa ya gaidata, sannan ya gaida Abba, duk suka yi shiru.

“Abba… Dama na zo ne in gode maku akan dawainiyar da kuka yi da ni, sannan in gaya maku dukkanin tunanina ya dawo. Zan sake sanar da ku har gobe bani da iyayen da suka wuce ku, ko babu komai kun soni, kun nuna mini gata.”

Abba ya girgiza kai,

“Ban cancanci ka yafe mini ba Muhseen. Na cutar da mahaifinka ta hanyar amincewa son zuciyar Bako. Na rasa yadda zan yi in roki mahaifinka.”

Ya fara kuka, hakan ya taba zuciyar Zayyad.

“Abba mahaifina ya yafe maka. Sannan ya amince a ci gaba da kirana Zayyad, sai dai ya sakani na yi takardu na canza sunan mahaifi na mayar da tasa sunan. Ya gaya mini ba zai iya jurar jin ana kiran dansa da sunan wani uban ba shi ba.”

Alhaji Salisu da mai dakinsa suka yi ta rokar Zayyad ya tabbatar masu da ya yafe masu. Sharifat ta karaso kusa da shi tana kuka,

“Don Allah Yaya kada ka nesanta kanka damu. Har yanzu muna kallonka a matsayin babban yayanmu wanda baya son kukanmu.”

Ya dago da jajayen idanunsa,

“Har gobe ku din kannena ne, babu abin da zai canza.”

 Anan ya zauna ya karya kamar komai bai faru ba, sannan ya dauki Sharifat domin ta je ta taya Samha aiki.

 Wannan abu ya faranta ran Alhaji Salisu.

A kwance suka sameta tana ta zazzabi. Da kyar ya lallabata ta amince ya yi mata allura, ya kawo mata tea tasha sannan ya ba ta magunguna.

“Sharifat ki kula da ita zan koma wurin aiki.”

“To Yaya adawo lafiya.”

Tun Samha tana nokewa, har dai ta saki jiki sosai suka yi ta hirarsu. Ta ji dadin zuwan Sharifat domin tare suka shiryawa Zayyad abinci.

<< Miskilin Namiji 22

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×