Ficewa ya yi ya nausa cikin dajin, hakan yasa ta fito ta nemi wuri ta zauna shiru tana nazarin maganganun da M.Y ya faɗa mata.
Yunusa ya ƙaraso tare da sallama. Dubansa ta yi cikin damuwa suka gaisa.
"Ina yallaɓai?"
Haka kawai ta ji haushin tambayar don haka ta haɗa rai ta ce,
"Ina zan sani.
Bai ƙara ce mata komai ba ya nemi wuri ya zauna.
"Kinyi dacen mijin aure."
Ya furta mata yana dubanta.
Ko tari bata yi ba, illa ma zuba masa idanu da ta yi tana jin kamar ta shaƙe shi. . .