Husna tana tsaye tana kallon irin wannan ƙauna da ke tsakanin Gwaggo da M.Y haƙiƙa idan ta gansu a cikin irin wannan yanayin nata iyayen sukan faɗo mata a rai, harma ta yi kuka. Allah kenan baya barin wani dan wani, da ya bar iyayen Husna ko dominta. A hakan ta gode Allah da samun uwar riƙo kamar Gwaggo. Kullum nuna mata take yi, bata rasa iyaye ba, ita ce uwarta ita ce ubanta.
M.Y ya ɗago suka haɗa idanu, irin kallon da ya yi mata yasa ta yi saurin barin wurin, dan. . .