A kiɗime ta ƙara cewa "ɓarawo, Innalillahi wa'inna ilahir raji'un ɓarawo a ɗakina, Meer rayuwata ɓarawo ya shigo mana" Babu wanda ya amsa Ridayya balle kawo mata ɗauki ta tashi zaune tare jingina da jikin bango, abu goma da ashirin ya haɗe mata. Ƴar raguwar wayar da ta yi mata saura a kadara itama an rabata da ita wai meke shirin faruwa ne. . .