Skip to content
Part 2 of 4 in the Series Muryar Dalili by Haiman Raees

Kirifto

1.

Assalamu Alaikum jama’a

Da fari da sunan mai sama

Al-Hadi Kai ne mai duka

Ka iya mana sarki Rabbana

Ka tsare mu sharrin aringizo.

2.

Gaisuwa mai tarin yawa

A wurin Habibu mai mu’ujiza

Annabi mai Makka da Madina

Shi ne gatan duka duniya

Manzonmu da babu kamarsa

3.

Dukiya ita ce jinin rayuwa

Da ita ake sarrafa duniya

Gwal ne ko kuma azurfa

Tagulla ce ko zubarjadi

Da Duk duwatsun alfarma.

4.

Ga dabbobi nan iri-iri

Harkar noma ce ga ta

Ko cinikayyar kayan sawa

Gona, gida ko filaye

Hannun jari ga masu da shi.

5.

Ƙarafan hawa dai ga su

Kayan amfanin yau da kullum

Kayan asibiti da na shago

Cinikayyar kayan karatu

Abubuwan dai ga su birjik.

6.

Hanyoyin samun kuɗi

Kamar duniya suna da faɗi

Akwai na haram da halali

Wani sai an nuna jan hali

Wani sai an yi fito-na-fito.

7.

Kwatsam kuma sai ga sabo

Al’amari sabo ya fito

Shi ne na haƙar Kirifto

Idan ka haƙa har ta fashe

Tabbas baki za ya washe.

8.

Idan ta maƙale kai ta zuru

Idanu su yi zuru-zuru

Ana ta jiran gawon shanu

Ana ta jiran shan man shanu

Wataƙila, ta hana bature ƙarya.

9.

Da yake haƙar ana samu

Wasu miliyoyi suke samu

Cus fa! Haka kuɗi ake samu

Sai dai mai rabo ke samu

Maras rabo yai ta jira.

10.

Wasu da yawa sun bar aikinsu

Wasu ko sun saki sana’arsu

Wasu sun bar aikin hannunsu

Sun ɗauki haƙar sana’arsu

Ita suka riƙe dare da rana.

11.

Abin na da ban mamaki

Kana zaune cikin ɗaki

Latsawa ce kawai aikin

Idan ta fashe kamar tafki

Kuɗaɗe sui ta shigowa.

12.

Lallai wannan ci gaba ne

Hanyar samun na kai ne

Kuma sauyin zamani ne

Za a rage talauci ne

Mutane za su samu sauƙi.

13.

Sai dai lamarin da jumurɗa

Malamai su na ta ja-in-ja

Wasu Kirifton sun ka haramta

Wasu shi ɗin su ka halasta

Wasu kuma suka ce la ba’asa.

14.

Daga cikin masu yin nazari

Sun ce a guji wani yanayi

Da za a ke samu a huce

Domin yana kashe zuciya

Da dakushe dukkan karsashi.

15.

To ni dai a ra’ayina

Kirifto dai ci gaba ne

Don haka zan yi abina

Ko da zan samu kaɗan ne

Na dai huce wa haushina.

16.

Aikin da nake yi na rubutu

Da aikin nazari da karatu

Na alƙalami da muryata

A tunanina da ƙwaƙwalwata

Su ma ba za na saki ba.

17.

Allahu ka sa mu amfana

Da ci gaban da ya zo mana

Wahalar mu ta yau ta zam hira

A wayi gari ba ma ƙara

Sai godiya da hamdala.

18.

Kiriftawa a dai yi hattara

Komai kafin yi a tsattsara

Wanda ba sa yi su fara

Allahu ya kiyaye hasara

Ya Zuljalalu Ya ba da sa’a.

 

 

<< Muryar Dalili 1Muryar Dalili 3 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
2
Free daily stories remaining!
×