Daga inda nake laɓe ina kallon danbarwar da ke faruwa tsakanin babana da matarsa wadda take cika tana batsewa tare da tsalle ta dire kan sai dai uban nawa yasan inda zai kai ni amma ba ta riƙe ni.
Ya share zufar da ke keto mishi da tsohuwar malum malum ɗin da ke jikinsa, ya ce "Yanzu dai ki bari zuwa sati ɗaya zan mayar da ita can Kaduna wurin abokan arziƙi da muka zauna tare za su yi min arziƙi su riƙe min Mai gadon Zinare."
Ta balla wa inda yake tsaye harara ta. . .