"Ta ina ta saci lambar waya a wayarki? Ai wannan da kike gani ita ce matarsa da ya rabu da ita mai ladabi da biyayya, mai son shi shi da kowa na shi. Matar rufin asiri."
Inna ce ta faɗi haka tana takowa zuwa inda nake.
"Kuna nufin ita ce mai gadon zinare da Hassan ke faɗi? Ummu ta yi tambayar cikin ruɗewa.
"Ƙwarai ita ce." Ƙanwar shi Ummi ta faɗi cikin tabbatarwa Ummu hani ta zube ƙasa ta fara birgima kamar yar yarinya "Wayyo na bani na kashe kaina."
Na tsallake su na fara takawa. . .