Ta tashi da sauri da nufin ta je ɗakin Zuwaira, sai dai duk yadda take tafiya sai ta ga ana dawowa da ita baya.
Zuciya ta dinga cinta, ta tsaya cak! Tana numfarfashi tana jin yau sai dai su yi mutuwar kasko ita da Hauwa. Dan haka ta juyo tana dubanta ido cikin ido. Duk da matsanancin abin tsoron da ke cikin idanunta hakan bai hana Munaya, zuba mata idanu ba. Suratul Rahman, take karantowa, cikin kuka da miƙa lamuranta ga Allah. Zuciyarta ta riga ta yi raunin da take hangen mahaifinta a matsayin matacce. Shikenan rayuwarta ta gurgunta. . .