Cikin kuka mai bayyana tana cikin masifar tashin hankali take roƙon Aunty Ladidi a waya don girman Allah ta taimaka mata, tazo gidanta da gaggawa a safiyarnan, tana cikin wani gagarumin bala'i ne da idan ba Aunty Ladidin ba babu wacce za ta iya fitar da ita a cikin wannan halin.
"Allah ya raba mu da bala'i"
Aunty Ladidi ta faɗa cikin rashin damuwa da irin kukan da Fatima take yi.
Daƙyar Fatima ta iya tsagaita kukan ta amsa da
"Ameen"
Ladidi ta gyara zama ta cigaba da cewa
"Maman Ummee (Inkiyar da suke ma. . .