Skip to content
Part 32 of 73 in the Series Sakacin Waye? by Sumayyah Abdulkadir Takori

Berom, sune kabilu na farko mafi girma da shahara a jihar Filato, tsakiyar Najeriya. Jos ta kunshi kananan hukumomi guda hudu wadanda suka hada da Arewacin Jos (Jos North), Kudancin Jos (Jos South), Barkin Ladi (Gwol) da kuma Riyom. Mahaifiya ta ‘yar Barkin Ladi ce mahaifina kuma dan Riyom ne. Su duka kananan hukumomi ne dake makwabtaka da juna. Mahaifa na sun hadu a chochi har soyayya ta shiga tsakanin su wadda har ta kai su  aure suka kuma haife ni. 

Saidai ban yi rayuwa mai tsayi tare da su ba, shekaru biyu da haihuwa ta suka yi accident ita da mahaifi na a kan hanyar su ta zuwa Barkin Ladi. Sai na koma hannun Kakata Veronica wadda ta raine ni a Riyom, amma mun tashi  acikin Hausawa sosai, daga baya GrandMa ta sayi gida nata na kanta a cikin kwaryar birnin Jos (Jos North) ta bar Riyom, ya zamanto cewa noma ce kawai take kai mu Riyoma  da Barkin Ladi.

Manyan kabilun Berom sune Iguta, Aten, Afizere, Ingwe, Atyap, Bajju, Ham, Jukun da sauran su. Iyaye na Jukunawa ne na farko wadanda sune kan gaba a kyawun surah a kabilar Birom bakidaya, amma bakake ne sid, masu asalin kalar kasar iyayen su Ethiopia.

Mutanen Birom suna da al’adu masu dadadden tarihi (rich ancient cultural heritage) da suke yi duk shekra, akwai bikin ‘Nzem Berom Festival’ da ake yi duk shekara a watan Mayu ko Afrilu, sauran festivities wato bukukuwan shekara na kabilar Birom sun hada da Nzem Touchun, da Wusal Berom, suna kiran Allahn su ‘Dagwi’ wato (Judeo-Christian God).

Bukukuwan nasu yawanci suna yin su ne a akan sha’anin noma da farauta wadanda sune manyn sana’o’I’in su da suke rayuwa a kai, suka kuma gada daga iyaye da kakannin su.

Ma’anar kalmar BEROM shine ‘Praise/Reward’. Wato “sakamako” da harshen hausa.

Hudowar addinin Christianity da zuwan ilmin bature ya canza da yawan al’adun da Beroms suka tashi dasu. Christianity and western education ya rage darajar addinin ‘Dagwi’ (Judeo Christian God) da Birom ke bi iyaye da kakanni. Ya kuma canza abubuwa da yawa na al’ada da muka tashi a cikin su. 

A kokarin manyan kabilar Berom na kada al’adun su su gushe gabadaya ne dalilin christianity and western education yasa suka kirkiri wani shahararren bikin “Nzem Berom Festival” wanda ake yi a kowanne satin farko na watan Afrilu. 

Nzem, lokaci ne da Biroms suke nuna mabanbantan al’adun su daga bangarorori daban daban na kasar Birom, musamman wake – wake da raye – raye (artifacts) da sauran al’adunsu. su.

Har zuwa inda yau ke motsi, Birom na matukar darajja bikin ‘Nzem Berom Festival’, kabilar Berom suna nan suna rayuwa a arewacin Filato duk da cewa a halin yanzu rikicin addini dana kabilanci ya durkusar da su  (kullum cikin tashin hankula suke), wannan ya karafafa zama  na a kasashen ketare, na kuma so in dauke Grandma mu zauna tare a duk inda nake amma ta ki. Ta ce mutuwa ce kadai zata raba ta da mahaifar ta wato Jos.

Kakata ta taba bani labari cewa a can baya ba addinin Kiristiyaniti suke yi ba, a shekara ta 1960 ne suka yi bakin Turawa, wato malaman addinin kirista wadanda babu inda basu kurda ba a jihar ta Filato, wadannan baki su ake kira da ‘yan Catholic ko kuwa Missionaries su suka tabbbatar da addinin kiristanci ya samu mazauni ga al’ummar Berom amma a baya suna bautar Traditional God ne ‘Dagwi’ (Judeo God).

Tun ina karami Allah ya hada jini na da ‘ya’yan Musulmi Siyam”. Ya bani labarin yadda ya samu sunan HAMZAH ALMUSTAPHA. A wannann ranar naji komai a kan Hamzah har abinda ban taba tunanin ji ba daga bakin sa. Ya ce “aure zamu yi Siyam, saboda haka we have to be open to each other. Shiyasa na gaya miki komai a kaina.

A dabi’a ta bani da saurin fushi, amma kuma ina da ruko. Kuma inna yi fushin bana sauka da sauki. Don haka in kin yi min laifi kin bani hakuri ban sauko da wuri ba kada ki damu, as time goes on zan hakura, saidai kafin na hakuran zai dauki lokaci.

Abincin da na fi so shine Tuwon Acca da Kunun Acca da kuma ‘Gwote’ wanda sune manyan abincin Beroms. Na san baki iya ba, ni da kai na zan sa apron in koya miki”.

Sai nayi murmushi, na mike na dauko tray din dana shigo da shi na kawo gaban shi na ajiye, na bude warmers din ina tambayar shi “ko shine wannan Mr. Birom Man?”

Da mamki yace “exactly tuwon Acca din mu kenan, maza zuba min Azumin Mambillah, sai yanzu na san ina jin yunwa!”

Sosai ya bani dariya don har da nannade hannun riga wato zai kwashi gara. Na zuba masa wanda na san yafi karfin cin sa. Hamzah yace “wannan mugunta ne, saidai mu ci mu biyu, kina bani a baki ina baki.”

Na saki serving spoon din akan tray na fasa kara masa naman dana yi niyyar karawa, ina cewa kaga Allah ka bari bana so, ni Baby ce da zaka bani abinci a baki?” 

Girgiza kai yayi cikin kallo na, yana fadin “ba zan baki amsa ba sai a lokacin da ya dace, lokacin da zan tabbatar miki keda Baby din da kike shayar min baku da maraba a waje na. Tunda kuwa har wanka Hamzah ne zai ke yi miki…..Ke kuma ki shayar da Hamzah tare da Babyn sa….”. Ya Ilahi, wannan karon cusa kai na yi a tsakanin cinyoyi na domin ba karamin kunya da nauyi kalaman sa suka saukar min ba. Shi kuwa ko a jikin sa, daga karshe yace “Allah ya kai damo ga harawa ko bai ci ba zai yi birgima iya son ran sa.

Na tara sha’awa mai tarin yawa Siyam, na yi hakuri mai yawa da maza iri na da yawa bazasu iya ba, na nisanci Zina don in kiyaye kaina daga dattin zina in kuma yi wa matar da na aura tanadi mai yawa. I hope zaki dubi hakan ki tausaya min, ta hanyar amsa kira na a kowanne lokaci na bukata, bazaki taba gajiyawa da yawan bukatu na ba, ba zaki yi amfani da wannan wajen hukunta ni in nayi miki laifi ba, kamar yadda I will make sure na tafiyar dake cikin soyayyar da ko a littafan hikaya babu, zan tabbatar na maida ke tauraruwa mai haske kuma abar envying a cikin mata ‘yan uwan ki saboda soyayyar da mijin ta ke yi mata. Zan yi duk wani aikin karfi da ilmi na don in tabbatar kin ji dadi a gaba dayan rayuwar ki ta gaba ke da ‘ya’yan da zaki haifa mun Siyam for your sacrifice for me, this is a promise!”

Sai na ji ni tamkar ina shawagi akan gajimare don dadi, ina kuma taya shi addu’a a cikin raina, kan Allah yasa kada mafarkan sa suyi nisan kiwon da nawa suka yi before actualizing. Ni kam na gama mafarkai, bani da tsari sai abinda Allah ya tsara min. Allah ya gama yi min komai tunda ya dawo da wanda zuciyata ke so zuwa siradal mustaqeem. So duk abinda zai biyo bayan wannan a gani na mai sauki ne,  ko yaya rayuwar zata zo mana a gaba zan jure zan kuma karbe ta muddin ina tare da Hamzah.

Yana cin abincin yana cigaba da bani labarin yadda ya samu kan sa a International Media bayan barin sa Jami’ar Sussex, ya gaya min ya taba yin aiki a Nigeria da wani gidan Radio na TRANQUIL a garin su Jos, da yadda a hankali ya koma BBC Hausa da Deustche Welle, kafin kuma ya dawo VOA. Da dalilan da suka sa mutane da yawa ke masa daukar cewa shi musulmi ne (wato kamannin sa, appearance din sa da Hausar bakin sa).

“Allah ya riga ya rubuta cewa ba zan mutu cikin bata ba shiyasa ya hada ni da ke Siyam. Matsala ta daya ce yanzu Grandma da kuma naki iyayen da yadda zasu karbi al’amarin mu.”

Hamzah ya fada cikin tausayin kai. Girgiza kai nayi, cikin gaskata kowacce kalma dake fita daga bakin sa.

“We have something in common Mr. Hamzah, nima ban tashi tare da mahaifiya ta ba, a hannun Kaka ta Ummati na girma. And she’s tough gaskiya, very tough old woman and very strong woman, nima ina shayin ta a kan al’amarin mu. 

Gara kai ka rayu shekaru biyu da mahaifiyar k ka sha Nonon ta kamar Ya Omar, ni kuwa sai a hoto na san fuskar Mamana, Kakar nan tawa ita ta shayar dani, don haka ita ce komai namu ni da Ya Omar”.

“Bani labarin Ummati da Yayan mu Omar.”

Sai naji hawaye sun cicciko ido na. Na ce “ban kyauta masa ba a kan ka, kuma dalilin sa na barin gida kenan don kada ayi min auren dole da shi. Omar mutum ne mara SON KAI. Yayi alkawarin taya ni neman ka, ban san meyasa bai cika wannan alkawarin ba. Ya zabi ya tafi ya bar mu gaba daya”, na share hawayen da suka fito min, sannan na cigaba.

         “Da wuya Umar yayi alkawarin da bai cika ba, don haka na san ba karamin uzuri bane ya hana shi dawowa a shekaru ukun da ya ambata, tunda dai Abba ya yi masa abinda ya ke so bai yi min auren dole da shi ba.

Shi din dan uwa ne irin wanda babu kamar sa Mr. Hamzah, kuma ba zan gushe ina yi masa addu’ar alkhairi da nasara a duk inda yake ba. Abinda ke damu na shine a wane hali yake?”

Hamzah yace “nuna min hoton sa, idan shi bai taya 8ki nemana ba, ni na yi alkawarin taya ki neman sa.”

Na soma lalube cikin gallery dina har na yi nasarar samo wani hoton mu ni da Ya Omar a kan tsaunin Mayo Selbe. Hamzah ya karbi wayar yana dubawa sosai, da wani irin mamaki, ya ce “I know this handsome face, kaman Faruk Gidado ko ba shi bane?” 

Wata irin zabura na yi na yi kan Hamzah ina fadi cikin  karaji “shine wallahi, sunan sa kenan na makaranta” na damki wayar daga hannun sa cikin zazzaro idanuwa na ina fadin “ka gayamin don Allah ‘Habeeby’ a ina ka san shi?” 

Hamzah ya kura min ido yana murmushi har sai da naji kunyar irin kallon da yake min da yadda nayi reacting kamar zararriya, ya ce “ta yaya zan yarda da cewa sabon sunan nan da aka kira ni da shi ba cin hanci bane? 

Shin an bani sunan ne baka da zuci? Ko kuwa cin hanci ne na nasan inda Omar yake? Tunda yanzu aka gama ce min Mr. Hamzah, aka ce Birom Man?”. Tafuka na na kai na rufe fuska ina ta dariya, na ce “ni bana bada bribe, ‘yar kasa tagari ce (good Nigerian citizen)” shi kuma ya ce “sai kin maimaita min sunan nan as bribe in kina so in kai ki gun Faruk Gidado.”

“A wata mas’alar malaami sun ce cin hanci yana halatta ai Habeeby”. Na fada with a very cool tone. Don dai in samu ya gaya min inda ya san Omar. Amma shi yadda na ke maganar kawai yake kallo a fatar baki na. Tsigar jikin Hamzah har tashi yake. Sai kawai ya mike ya ce “gara in tafi kafin yarinyar nan ki lalata hakuri na da jajircewa ta.”

“Kada kayi min haka Habeeby….don Allah ka gaya min a ina Ya Omar yake? A ina ka san shi?”

Hirar nan bazata yiwu ba Siyam, gara in tafi sabida ina cikin wani hali. 

Ki daure gobe ki je office zan gan ki a can, ba zan kara yarda mu kadaice ba sai kina a matsayin mata ta.”

Kamar zan yi kuka nace “kana ta kaucewa abinda nake son ji? Kana gaya min mara amfani.”

Cikin mamaki yace “ina gayami miki tawa damuwar saboda kowa akwai abinda ya dame shi, kina ce mata mara amfani? Well, na fahimce ki. Kina son in dawo miki da tsohon saurayin ki ku hadu ku hade min kai, ku gaku ‘yan gida daya alhalin ban riga na kama dahir ba ko?”

Mr. Hamzah ya fada murya da idanu duka cike da kishi mai tsananin gaske. Bansan sanda na yi dariya ba, nayi na sakeyi har da sunkuyawa na ce,

“Ka yi wa Allah ka gaya min ko da fatar baki ne. A ina Ya Omar yake zaune? Idan baka sani ba shine mutum na farko da zai tsaya tsayin daka wajen sawa Abba ya yarda da auren mu, saboda Abba baya tsallake maganar dan sa Omar.”

Ai jin haka yayi maza ya ce “yana kasar nan, ma’aikacin bankin Morgan Chase ne, na san shi mun saba ne a dalilin a can ne salary account dina yake. Idan ina da matsala ta banki wajen shi nake zuwa. 

He’s a very smart guy and yana rayuwar sa freely ban ga alamun wata damuwa a tare da shi ba.”

“Can I hug you  Mawonmase?”

Na fada cikin hawayen da suka tsatstsafo mini. Sai yayi dariya ya juya yana tafiya zuwa kofa.

“Domin ka bani albishir din da wani bai taba yimin irin sa ba, albishir din dana ke da tabbacin shi zai shirya ni da Abba na, idan na cika alkawarin dana yi masa na nemo masa dan sa Omar.”

Na fada cikin hawaye. Hamzah ya juyo gabadayan sa ya bude min hannuwa ya ce “hug me if that is okay with you” kunya mai tsanani ta kama ni, na dauki throw pillow na kujerar falon na jefa masa, ya kama da sauri ya rungume kai kace Siyam din ya runguma, yace.

“Allah ka bani Siyam a gida na kafin watanni uku.”

“Balle ma ba za’a kai ba tunda ka nemo Ya Omar, ka sa a ranka aure ya zo. Kawai ka kai ni gare shi.”

“Abban mu (Young Abba) ya ce kada in kara daukan ki a mota na sai bayan na biya sadaki. Bai yarda ba, bai amince ba, don haka gobe after office sai mu wuce har Antin ki a tata motar, sai ku bi ni a baya.”

“Lokacin kuma ai shima ya tashi daga nasa aikin, ko ka san gidan sa ne? Ai gara mu je da safe ido na ganin ido.”

“Alright Habeebty, mu kwana lafiya, a cigaba da mafarki na, but please this time around kina hadawa da kyakkyawar sumba a kowanne mafarkin,  I’m sure zata iso gare ni tunda nima yanzu kullum na kwanta sai nayi mafarkin ki”. “Kai Hamzah!” Na fada ina rufe fuska, abinda bai sani ba har wankan janaba sai da nayi a kan mafarkan sa.

“Ina son sunana HAMZAH…Amma daga bakin ki na fi son wancan, dan sake fada min?”

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 3.8 / 5. Rating: 4

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Sakacin Waye? 31Sakacin Waye? 33 >>

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×