Duk sai suka yi shiru, kowanne na jin nauyin dan uwansa, ya rasa daga ina zai fara.
Na kawowa Ya Omar shayin sa da na kammala hadawa na juya zan wuce toilet don yin alwallar la’asar, Ya Omar ya ce, “Boddo am, nonnon be jabata kodo? Do na tarbiyya je be wanni ma ba. Kodo kam handanai ni sam ha amin sakko gorkoma” (haka ake karbar bako? Wannan ba tarbiyyar da aka yi miki ba ce. Mu bako abin darajjawa ne da girmamawa a gare mu ko wane ne, balle mijinki).
Zumbura baki na yi, ni ma na mayar. . .
Good