Wuya sosai ta sha hannun Abdurrashid har sai da ta fara mishi kuka ya sarara mata.
A jikinsa ya rungume ta hannunsa kan cikinta cikin kunnenta yake raɗa mata zancen cikin Aunty Karima, buɗe idonta ta yi daga lumshe sun da ta yi ko da Aunty Karima ta tashi daga ganin abinci ba ta kawo ciki ne da ita ba ta taya Auntyn murna a ranta.
Hira suke a hankali har sai da aka kira sallar magrib ya raba ta da jikinsa ya shiga bathroom.Ita ma anan ɗakin ta yi sallah don ba ta gyara ɗakinta ba. . .