Nafisa ta tarar da Maryam a tsaye kan Zainab tana kukan makirci, da sauri ta miƙa mata katin hannunta na rawa.
“Anty Maryam kin san me na gani yanzu a waje yana faruwa?”
Maryam ta dakata da loda katin wayar ta bayar da hankalinta ga Nafisa idanunta a waje.
“Wai wasu yara ne suka tsinci jariri a baƙar ledar an yaddar a bola… sai na ji tsoro na ga kamar jaririn da Anty Zainab ne kikace ta yi ɓari…”
Cikin bayyanannen tashin hankali Maryam ta iso ga Nafisa jikinta na rawar mazari.“Ke…! Ke ba shi… ba shi. . .