Skip to content
Part 25 of 25 in the Series Sirrina by K_Shitu

Wasa-wasa tun Aliyu na ɗaukar jikinta da rashin sabo har ya fara tsorata, wani irin zazzaɓi take yi da ciwon kai, kullum cikin shan drip take, ta yi wata irin rama, hankalinsa ya kai ƙololuwa wajen tashi, tun yana ɓoyewa har Ammaah ta fahimci halin da suke ciki, daga ƙarshe da abun ya tsananta Part ɗin Ammaah aka mayar da ita, ita ke kula da ita, ga wani irin mugun haske da ta yi sai idanuwa da karan hanci kawai ta faɗa sosai, idan ka kalle ta dole ta baka tausayi. Tamkar Aliyu ne ke ciwon shi ma duk ya fita hayyacinsa. Wani so da ƙauna yake yi mata, har baisan adadi ba, ko da yaushe yana Part ɗin Ammaah, ko magana ma da ƙyar take yinta.Ita kam Aaliyaah tun da ta fara shan maganin da doctor ta bata abun ya same ta, sai ciwon jiki da jigatar da ta yi wajen Yarima suka haɗe mata.

Kusan Sati uku kenan abu ya ƙi ci, ya ƙi cinyewa. ana ta nema mata magani babu ci gaba, sai ma aman baƙin jinin da take yawan yi cikin kwanakin. Sai da ta yi wata Biyu tana jinya sannan Allah ya kawo mata sauƙi, cikin kwanaki biyun da yarima ya yi tafiya ta ji sauƙi ta yi wata ƙiba, ta yi ɓul-ɓul ta ƙara kyau.
Ɓangaren Amarya mufeeda ma babu wani ci gaba, dan Yarima ya buge mata warning ko ganinshi ta yi kar ta sake ta ko fito, tsananin tsoron shi da take ji ya sa ta shiga taitayinta.

Zaune Aliya take Parlourn Ummi tana Kallon Tv ta yi kyau cikin Lifayar da ta sanya golden, cike da zumuɗi ya shigo Parlourn. Harɗe hannayensa yay a ƙirji yana kallonta ya yi kusan 5mnts a haka sannan ya tako cikin nutsuwa ya iso inda take hankalinta gabaɗaya yana kan tunani ba ma film ɗin take kallo ba.
Kiss ya sakar mata a goshi, a razane ta fasa ihu tana runtse idanuwa, cikin shagwaɓaɓɓiyar murya ya ce, “Haka ake tarbar miji??” a hankali ta buɗe idanuwan ta kalle shi, sai kuma ta turo baki ta ce, “Shi ne zaka bani tsoro ko na yi fushi”. ya zaro idanuwa ya marairaice, ya fara roƙonta har ta haƙura.

Ammaah ce ta gito ta ganshi, ta haɗe fuska ta kalle shi tana nuna masa ƙofa da hannu ta ce, “Tashi” zaro idanuwa yay ya ce, ”Why Ammh??’

Ta harare shi sannan ta ce, “Daga dawowarka zaka danne ta kana ganin yanda take fama da jikinta.” Turo baki yay ya ce, “Wallahi Ammh na gaji da yawa shi ya sa”. ya ƙarashe maganar yana miƙa, pillow ta ɗauko ta nufo shi da shi, da gudu ya tashi ya fice ya ɗaga murya yana faɗin, “Please ki kular min da wife”.

Sati ɗaya da dowowar shi ya fitini, Ammaah yana so Aaliyaa ta koma sashen sa, amma Ammaah ta rufe ido ta ce bata san zancen ba.

Haka suka ci gaba da rayuwa cikin kwanciyar hankali, sai dai damuwar Yalaaz na laƙahe a zuciyar Aliya, ta daina Amfani da wani abu na tsafi shi ya sa bata san halin da suke ciki ba.

Ana cikin yanayin, Ammaah ta bada shawara ya mayar da ita school, aka yi mata komai ta fara zuwa University…wata uku da fara zuwanta, Ciki ya bayyana ƙarara, sai wani mugun kyau da ƙiba da ta ƙara ga kwaɗayi da yawan bacci, da kuma masifa.

Lokacin da suka fahimci cikin farin ciki kamar su yi hauka, me martaba ya basu kujerar makka, suka nufi ummara, sun daɗe kusan 25days suka dawo Aliya ta ƙara kyau ta yi gwanin burgewa, larabawa sai hauka suke yi kan Yarima amma Aliya ta rufe ido ta zazzaga musu raahin mutunci na ƙin ƙarawa.

Sai da Cikin Aliyerh ya shiga 8months sannan ta daina zuwa school, cikin ya yi wani irin girma tayi nauyi sosai.

Wasu na farin ciki da mata addu’ar sauka lafiya wasu kuma baƙin ciki kamar ya kashe su.
Cikinta na da 9months da 3days Aka fitar da ita India, a chan a haifi Twins ɗinta masu wani irin kyau mashAllah, kamar aljannu, sai shegen wayau.

An dawo Jordhaan an yi suna na gani na faɗa, baban videon da ya yi ta trending a social media videon ranar suna da aka baiwa Yarima Microphone aka ce ya faɗi wata kalma guda ɗaya ga matarsa, ya ce “I love her….she’s my secret she’s, my heart beat, she’s my life partner, she’s my Noor…”

Wannan Videon shi ya fi, ko wane kashe mutane, Namijin da ke da tsada ƴan mata, suke hauka kansa amma basu ishe ahi kallo ba shi ne ke zuba haka, sai sanyin matarsa ake yi itama.

Ɓangaren Mufeeda tana cikin tashin hankali, saurayinta yana mata barazana da wani videonsu da suka baɗala, akan sai ta bashi 80millns, ga shi taƙi faɗa wa kowa, ita aurenta ma da Yarima ya yi ma rahama ne a gare ta ko ba komai ta fito Mrs Aliyu Muhammad Ali.

Twins ɗin su Aliyaa ma sun girma sun kai 3months kyawawa yara sai ɓarnar tsiya da wayau.
Muhammad (hammad) sai A’ishatu (Noor), Aliya ta ci gaba da karatunta fannin Doctor cikin kwanciyar hankali, dan yaran Ammah ke kula da su, Kaf masarauta, babu yaran da ake ji da su irin Noor da Hammad.

SANAAM ta sanarwa Aliyaa Abubuwan da suka faru ta madubin toilets da ta haɗa, sannan kuma Aliya ta bata labarin Addinin musulunci da kuma Yaranta, ta kuma yi mata alƙawarin zata inshAllah.

Kwanaki biyu da suka yi wannan wayar, take sanar da Yarima tarihinta kaf, ya rungume ta sosai yana farin ciki, ya ce, “A-S (Aliyu’s-Secret) ya kama ta ke ma ki huta kin sha wahala sosai”. daga time ɗin ta kwashi yaranta suka yi bankwana a Jordhaan zata je, masarautarsu.

Da tsun-tsun Sanaam da ta hau ya ɗauke su zuwa Yalaaz. ta koma chan sun tarbe ta hannu bibbiyu, sannan kuma ta sha baƙar wahala kafin su yafe mata, daga nan ne ta fara chusa musu addinin har sanaam ta amshi muulunci sai kuma Sarauniya Saraah, da kuma ƙarfin Khaal bamanul Ansar da ya hana duk tsanani su ƙi yin yaƙi na uku, aka samu salama ba a yi yaƙin ba.

Da baƙin ciki ya taso Sahash da Sarauniya kunjam sai suka nemi halaka yaran Aliya, amma ta watsa musu ruwan addu’a lokacin da ta gansu, dukansu jikinsu ya ƙone ya saɓule ba kyan gani, suka barta, suka fara muguwar jinya ba magani.

Saboda Halaccin Ammaah ya sanya ta mayar wa Mahaifiyarta suna A’ishatu.

Sarki Zahir sun riƙe Aliya tsawon Wata biyu sun hana ta komawa Jordhan duk ta damu ga shi ba alamun service bare suyi waya da Yarima.

Sahash tana da suna Khadijatu, sai Risha da take da suna Zainab, sannan kuma ja gaba tsoho Arar da ya koma Ibrahim Khalil.

Sahash da Kunjaam sun zama ababen ƙyamata babu me iya matsawa kusa da su saboda wasu tsutsotsi da ke fitowa jikinsu, an yi magani amma ba sa’a.

Fahimtar da Mayun suka yi cewa Wasunsu sun fara barin addinin su, suka taso Aliya gaba.
Ta sha wahala sosai kamar zata rasa Rayuwarta.

Sai dai babu Ƙarfin sihirin da yay tasiri kanta, hakan ya sa suka saduda, ga kuma ƙan Lu’u-Lu’un Rauhanai da ta samu a ɗakinta ta mallaka musu shi daga nan suka bar yalaaz amma Lazaan ya amshi musulunci ya kuma samu ilimin addini sosai wajen Aliyaa. Daga nan Rauhanan Suka fara musulunta suma.

Daga ƙarshe bayan gwagwarmaya da shan baƙar wuya, AZLAA ta amshi addinin Allah ta koma Hauwa Mai jidda, sai kuma RIYAD Abdullahi, sannan ja gaba NAZAAN Wanda ya koma Muhammad.

An samu Ci gaba sosai, da zaman lafiya saidai kuma su Sahash da suke cikin mawuyacin hali, sun rasa ganinsu, Sarauniya Halsha ta musulunta cikin gaggawa ganin irin bala’in da ya fara samun su Sahash, Sarauniya Rahash kuwa an nakasa ta dan bata da ƙafafuwa.

Firaish kuma Su Laila da mahaifinta sun masa kisan wulaƙanci an bar kanshi a yalaaz kowa na gani, sarki ZAHIR ya koma ALIYU bisa zaɓin da Aliya ta yi masa na suna.

Watanni shida Aliya ta yi, An samu muhimmin ci gaba a Yalaaz, tattalin arziƙi ya ƙaru. Azlaa da Nazaan Riyaad duk sun sauka daga mulki, sun barwa sababbin adalun sarakuna, Amma Sarki Zahir shi ne dai har lokacin, duk wani azzalumi makwaɗaicin mulki sai da ya girbi baƙaƙen d’abi’un da ya daɗe yana aikatawa. Mufeeda ta samu matsalar ƙwaƙwalwa, ga shaye-shaye da yay mata illa, ga kuma maƙasudi, na Videonta na tsiaicinta suna baɗaka ita da Jabir saurayinta, sai kuma sakin da yarima ya yi mata, hakan ne ya sanya ta zare ta shiga tona musu asiri ita da uwarta akan sune suka kashe Mariganyiya Khadija ƙanwar yarima Aliyu, da gudummuwar Sarauniya Bilkisu sai kuma, Momma da galadima, kowa ya girgiza da jin Al’amarin duk akan jin sirrinsu da tayi tana kuma ƙoƙarin tona musu asiri akan Ƙungiyar safarar ƙoyoyi, da gurɓatattun magunguna da suke da ita.


*****

BAYAN SHEKARA BIYAR.
Dr. Aleeyer Aliyu Muhammad na da shekaru 28 a duniya, da kuma yara biyu mace da namiji, sai A-s ɗinta Dr. Aleeyou Muhammad Ali. mai shekaru 37, wanda duniya ta sani sun yi fice sosai da shi da Matarsa aun buɗe Asibitinsu _A&A Da A-S Sai A-M&A-A_ A&A Aliyu da Aliya, sai A-S Aliya’s Secret, AM&AA A’ishatu Amaah da Me martaba Muhammad Ali. sai AA A’ishatu Mahaifiyar Aliya, sannan A Aliyu Me martaba mahaifin Aliya. Sai haɗaɗɗen masallacinsu tsadadde mai kyau wanda aka narka dukiya, da kuma gidajen Marayu biyu, sun yi aiki sosai, sai san barka.

Sanaam da Yusuf Ƙanin yarima ma sun yi aurensu da yarinyarsu ɗaya Hauwa. Sai kuma Zainab (Risha) da Aminin Yarima Abdullahi.

Yalaaz an samu ci gaba, Sarakunan sun yi amfani da tsananin dukiyarsu sun yiwa ƙasar hidima, an samu malaman addini sosai, ilimin boko, wutar lantarki, asibitoci, makarantu, har da haryar jirigin sama da na ƙasa, ga tattalin arziƙinsu na noma da yawan kiwo da ya bunƙasa. kowa ya wadata da addinin musulunci, kaso 90% cikin ɗari na mayun sun komo mutane kuma musulmai. har Ƴaƴan Aliya ma Mutane na.

Dr Khadija Muhammad shitu ma, ta bada tata gudummuwar sosai sun zama aminnan juna da Aliya duk da shekarunsu, sun zama mata masu aji da ji da kansu, ga wayarwa da al’umma kai da suke yi, ita ma Doctor tana da yara uku. mata biyu namiji ɗaya.

Azlaa ta rasu sannan Tsoho Arar Aliya ta yi kuka sosai ta ji mutuwar har ta haƙura ta koma yi masa addu’a, zumunci sosai ke tsakanin JORDHAAN DA YALAAZ. Sahash kanta ta amshi musulunci, ta auri Tazaan.
Sun samu aminci tsakaninsu da Aliya sai fatan alkhairi kowa ke yiwa Aliya.

Aleeyer ce kwance bisa cinyar yarima yana shafa kanta suna fira, ta tashi ta zauna sannan ta tambaye shi ta gama rubuta labarinsu tsaf wane suna yake so, buɗar bakinsa kawai sai ce mata ya yi, Sirrina. Bata ja zancen ba saboda tsananin soyayyar da ke tsakaninsu duka abun da yake so tana so, wanda take so yana so Labarin Tarihinsu ya zama Sirrina!!

Wata irin soyayya Aliyu da Aliya ke yiwa juna mai tsayawa a rai da ruhi mutane da dama sun san irin yanda suke tsaftattaciyar rayuwa me cike da tsantsar ilimi da kuma alkhairi, da daraja da kuma imani.

Lokacin da Marubuciya Aleeya Aliyu Muhammad ta kammala littafin sai Dr K_shitu ta ɗauki nauyi ta buga shi, A 2023, Littafi ya yi farin jini sosai, duk lokacin da aka tambayi menene ya kawo Sirrina amsar; Zaɓin Sirrin Aliya, Aliyu ne.

Sun faɗakar ita da Dr K_shitu, sosai ga Al’umma akan sihiri ba daidai ba ne, da kuma shirka, duk mai aikata su ya halaka ba shi da rabon duniya da lahira idan har bai tuba ba.

Ita ma Aliya lokacin hutu da kwanciyar Hankali ya zo Mata Allah ne abin godiyarta, kuma ta tsare ibadarta, da mijinta duk irin arziƙinta bai hana ta yiwa mijinta komai ba, ita ke masa girki da duk wata ɗawainiya tashi ga son junansu da Noor & hammad ke yi, suna ƙaunar iyayensu Hammad ɗan gidan Aliyaa sai Noor ta wajen Aliyu.

ƘARSHE.

ALHAMDULILLAHIL LAZI BI NI’IMATIHI TATIMMU SALIHAT.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 1 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Sirrina 24

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×