39 DAYS AGO!
Gandun Albasa. Gidan shiru, gaba d’ayansu suna zaune kowa yayi jugum!Kamar a nan ake zaman makokin.
A hankali Shuwa ta juya ta kalli Ummu kafin tace “Gaskiya fa Mama ta fad’a Ummu, ku je kawai ke da Sakina. Ai ta ce ta kirashi ko?”. A hankali Mama ta d’aga kai alamun ‘eh’. Ajiyar zuciya Ummu ta sauk’e kafin tace, “To shikenan Hajiya. Sakina taso mu je,Babanku yana waje.”
A hankali Sakina ta d’an kalleta sai kuma ta d’auke kai tace “Ummu, dan Allah ki je kawai ko. . .