Da idanuwa Aisha take binshi tunda ya koma asibitin, tana zaune akan gado ta mike kafafuwanta, da kofin shayi a hannunta da take kurba a hankali saboda zafin shi, yanayi mata dadine sosai, saboda ya sha kayan kamshi, kuma data tashi hadawa sai bata saka madara ba, ta zuba Milo mai yawa dan ko sikari bata saba. Yayi sallama, ta amsa masa, bai kuma kalleta ba, ya karasa yaja kujera ya zauna. Fuskarshi take kallo, gabaki daya kamar shine yake jinyar, yayi wani irin zuru-zuru da ko a lokuttan rashin lafiya bata taba ganinshi haka ba.
"Me kaci. . .
Thank you