Tunda ta fara magana suke kalonta, tabbas ta kawo shawara kuma dole da ita zasu yi amfani.
Mami tace"Ina tunanin in komai ya lafa zamu bar garin nan har kai Sunusi saboda kar makiya su gane domin duk wannan rufa -rufar yanzu na gane tana da wa'adi dole wata rana a gano mu".
Ajiyar zuciya kawu yayi yace "shikenan Maman Safwan Allah ya rufa asiri bari na tafi duk abunda yake da akwai sai aimin magana in ta kama mubar garin yau a shirye nake domin mutanan nan basu da imani".
Cikin rauni ta amsa da amin ya. . .