Bayan masu kawo lefe sun watse ne kasancewar a dangin Faruk mutum uku ne kawai suka kawo sai maƙotan su kawu da suka shirshigo, yawan kayan yasa da yawa suka dinga fita suna dawowa da wasu dan kashe kwarkwatar idanunsu.
Akwatu uku ƴan uwa suka juye da sunan wai zasu raba tsakanin su, haka akasa empty akwatu da sauran kayan a dan sahu dan kaiwa gidan su Ummu bayan watsewar kowa.
Ummu bata nan Sai Hajiya kawai, da ƴan biyu, ganin cikin wasu akwatunan babu kaya sai Hajiya ta tsorata dan tasan zuciya bata da kashi, kar ta fa. . .