Washe gari da wuri Faruk yazo dan suje asibitin, kasancewar tun jiyan ta sanar da Hajiya ita kuma Hajiyar ta ce su tafi da Aisha ko Sadija duk da cewar an ɗaura musu aure anma tunda ba kowa ya sani ba kamar mutan unguwa tafiya da ɗaya daga cikin nasu zaiyi kyau.
Tsaf suka shirya duk su biyun sun yi kyau, duk da kasancewar Sadija ƙarama anma kyanta ya gama fitowa dan tafi Ummu kyau sai dai kawai Ummu ta fita kwarjini.
Yana tsaye jikin motar sa, ya zubawa ƙofar gidan nasu idanu hannayen sa harɗe kan ƙirjinsa yayi. . .