Suna ƙoƙarin kamata su fita, Inna ta ga alamun haihuwa ta ce, cewa tai da Ummu Hani ta yi maza ta kira mata matar nan jami'ar asibitin, to kawai Ummu Hani ta ce, ta miƙe a hanzar ce, ko tsoron masifar matar babu aranta.
Matar har ta fara bacci Ummu Hani ta taɓa ta, kamar ɗazu cikin masifa take faɗin “Malama lafiya bana ce muku ni bazan iya komai ba?”
Kuka sosai Ummu Hani tasa.
“Dan Allah nurse ki tai maka, kizo.” Shiru matar ta yi kamin ta yi tsaki, ta miƙe
“Muje” shine. . .