Zaune suke Fatima na doguwar kujerar dake ɗakin inda Ummu ke zaune kujerar dake kallon Faruk suna hira kasa wannan ya kara batawa Fatima rai ta mike a fusace zata bar ɗakin Faruk na kallon ta har ranta Ummu taji daɗin haka sai dai me ji tayi Faruk na faɗin,
“Ummu dan Allah ɗan bamu guri zamuyi magana da Fatima.” Ranta ne ya baci ta dubi Faruk din sai ta kasa magana dan ya mata kwarjini kwafa kawai tayi ta bar dakin ranta na mata suya sosai haka kawai taji bata son Ayatullah ya ganta cikin ɓacin rai. . .