Kai tsaye asibitin suka wuce da musa, office ɗin likitan suka wuce batare da wani biye biye ba, dan su Faɗawa likita ga Musa yana so su gwadashi.
Ba ƙaramin tashin hankali Ummu ta shiga ba, da likitan ke faɗa musu sai dai suyi haƙuri Allah yaima Umma cikawa, kukanma kasayi tai, baby ɗinsu ta amsa ta rugumeshi cike da tausayi.
Da taimakon likita, da su Musa aka basu gawarsu suka yo gida da ita, Ummu gani take kamar Umman kawai bacci take, tama kasa yadda da cewar wai Umman gawa ce.
Kusan da asuba suka dawo. . .