A falon da na fi zama muka zauna su kuma ba kowa a wanda suke zama. Vicky ta yi ta karakainar jera mana abincin, Nabila da ta yi tsit tana kwasar gitki sai da ta cinye na gaban ta ta ajiye cokalin ta dube ni "Ke haka yarinyar nan ke ba mijinki abinci?
Na ce "Mene ne? Ta ce "Ta gwanance, kina zaune yana cin abincin wata?
Na narke fuska "Kin san uwar kasalar da nake ji? Allah wanka ma da ƙyar nake yi."
Ta jinjina kai "Kodayake burgewar auren manya kenan ka yi ta zuba shagwaɓarka ana. . .