Skip to content
Part 16 of 18 in the Series Warwara by Haiman Raees

Ke Ce Ta Daya

Na zamo ɗan biri, 

A fagen soyayya 

Bishiyar so na hau, 

Har ina juyawa. 

Bani jin ko jiri, 

Sai ka ce jariri, 

Gani a sarari, 

Amma bani nan a zahiri. 

Na zamo hankaka, 

‘Yar wani zan ɗauka. 

Kan sonta nai hauka, 

Ga zuciya na kuka, 

Ke ce ta ɗaya a komai,

Ke ce ta ɗaya a komai. 

Ke ce nake so tabbas, 

Ke ce nake da tabbas. 

Ke ce kika ce min ass!, 

Amma na kasa kataɓus. 

Don ke ce ta ɗaya a komai. 

Ke ce ta ɗaya a komai.

Ke ce muradin ruhi,

Ke ce buƙatar ruhi. 

Ke ce tunanin ƙalbi,

Ke ce a kullum zan bi 

Ke kin ka zamto komai,

Ke ce ta ɗaya a komai.

Ke ce na ba wa sirri,

Ke ce nake ta buri.

Akan ki nake ta kuri,

Har anai mini kirari.

Don ke ce ta ɗaya a komai,

Ke ce ta ɗaya a komai.

Zuciya har jini,

Ke ce a gare ni.

Ki kasance da ni, 

Kar ki guje ni. 

Zan iya rabuwa da kowa, 

Zan iya rabuwa da komai. 

Domin na baki komai, 

Saboda ke ce ta ɗaya a komai.

Bookmark
ClosePlease login

No account yet? Register

Rate the story.

Average: 5 / 5. Rating: 1

As you found it interesting...

Follow us to see more!

<< Warwara 15Warwara 17 >>

2 thoughts on “Warwara 16”

Drop a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You cannot copy content of this page.
3
Free daily stories remaining!
×