Har cikin gidan aka musu jagora, a wani haɗaɗɗen palour aka sauƙe su, Mami har lokacin bata daina hawaye ba, dan abubuwa da dama suna dawo mata sabo fil, musamman rashin ƴan uwanta ƴan biyu, da kuma rashin Ummanta, wa ya sani ko ƴar Adda Habiba tana nan ko ta yi aure ma, so take kawai ta kalleta, ta kalli yacce takwarar Ummanta ta girma.
Matan Sarki dukka an sanar da su, kamun ka ce me ma duka masarauta ya ɗauka da maganan dawowan Gimbiya Ramlatu, bayan shekaru ashirin da barinta gida.
Daga hadimai har dogarai, duk. . .