Komawar Zubairu Makaranta sai abubuwwa suka sake rincabewa. Ashe dama sun bari ne don sun gane yana kai kararsu wurin Babansu.
To yanzu ba ya nan sun ci gaba daga inda suka tsaya. Sai dai Ziradat ta riga ta tsorata saboda dukan da Baban ya yi mata a kaina.
Zainab ce take nuna mun salo iri-iri na rashin kunya da kuma nuna isa, amma na danne zuciyata ko kallon iya-shegenta bana yi.
A daidai nan ne kuma wani sabon laulayin ya kama ni, watanni uku bayan barin da nayi.
Amma a hakan na tsaya tsayin daka wajen ganin. . .