Sai lokacin da na saba shiga kitchen na fito na kama aikina.
Sai kuma wurin cin abinci muka ga juna da Aunty Farha, washegari kuma dole ta shiga kitchen abin da ba ta yi a gidanta ga Madam Hajjo a gefen ta.
Ni sai na bar mata ma gidan, gidan Hafsa na shiga muka tafi gidan Khadija muka yi hirar mu sai yamma sosai na dawo na kuma shige ɗaki.
Ko da suka zauna cin abinci ban fito ba ta waya ya kira ni na fito na ci kaɗan don na ci abinci gidan Khadija.
Da safe ina shirin. . .