A hankali magana ta shiga kunnen ma fi yawan kusanci da Fatima, da yawansu Allah Ya kara suke mata, da fadin wai dama wana kambun maza ne, ka gama shan wahala dasu daga karshe su suka maka da kishiya.
Fatima kam ba ta san abin da yake faruwa ba, harkar gabanta kawai take yi, musamman yanzu da suka hada hannu da Ummi suna kasuwanci hijabai dinkakku da kuma dogayen riguna. A bangaren Mustapha kam ba ta da wani kuka in yanzu ta ce wash zai ce menene, idan bai magance ba, to tabbas baya da shi ne.
Maganar zuwa Maiduguri. . .